Addinin Musulunci da Kiristanci
Ba dukkan ƙasashe 206 na duniya ke bikin Kirsimeti ba, duk da cewa ana shagulgulansa a ƙasashen Kirista irin su Birtaniya da Amurka, har ma da wasu ƙasashen Musulmi.
Bincike ya nuna cewa babu wata doka da aka tanada a sababbin dokokin haraji da ke nuna cewa an ware musulmai, ba za su rika biyan haraji ba a Najeriya daga 2026.
Amurka ta bayyana cewa ba za ta tura sojoji zuwa Najeriya ba, tana mai cewa sanya kasar cikin jerin CPC hanya ce ta diflomasiyya don karfafa gyare-gyare.
Tsohon gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya bayyana cewa shugabannin da ke cin amanar da Allah ya ba su, za su dandana kudarsu a wurin Ubangiji ranar Lahira.
Kungiyar hada kan 'yan Arewa ta NRG ta kai ziyara ga shugabannin Musulmai da Kiristoci na JNI da CAN domin kara fahimtar juna a Arewacin Najeriya.
Wasu rahotanni sun yada cewa Hukumar DSS ta cafke malamin addinin Musulunci a jihar Osun bayan yada bidiyonsa yana zanga-zanga kan Falasɗinu amma ya karyata hakan.
Ana sa ran Najeriya za ta ayyana hutun Kirsimeti, Boxing Day da sabuwar shekara na Disamba 2025 da Janairu 2026, inda ake sa ran za a rufe wuraren aiki.
Gwamnan Ebonyi, Francis Ogbonna Nwifuru, ya amince da biyan ₦150,000 a matsayin alawus din Kirsimeti ga dukkan ma’aikatan gwamnati a jihar gaba daya.
Kungiyar Equipping The Persecuted ta yi gargadi kan yiwuwar hare-haren Kirsimeti a Arewa, DSS ta tabbatar da daukar matakan kariya yayin da ake shakku kan zargin.
Addinin Musulunci da Kiristanci
Samu kari