
Yan jihohi masu arzikin man fetur







Fitaccen lauya a Najeriya, Femi Falana ya ce marigayi tsohon shugaban kasa, Umaru Yar’Adua ya soke sayar da matatar mai ta Port Harcourt saboda rashin bin ka'ida.

Kamfanin mai na kasa ya bayyana irin manyan nasarorin da ya samu ta fuskar farfado da matatun mai na Warri da Fatakwal, an fara gyaran ta Kaduna.

Gwamnonin jihohin Rivers da Bayelsa sun kawo karshen rikici kan rijiyar mai da aka shafe shekaru 22 ana yi a tsakaninsu wanda suka yi yarjejeniyar janyewa daga kotu.

Har yanzu ba a fara sayar da fetur a kan N935. Kungiyar dilalan man fetur ta yi bayanin jinkirin da aka samu. Amma ta fadi lokacin tabbatar da sabon farashin.

Kungiyoyin fararen hula sun hada tawaga ta musamman mai mutane 50 domin gano gaskiya kan halin da matatar NNPCL ta Fatakwal ke ciki ga yan Najeriya.

'Yan Najeriya za su fara cin moriyar ragin farashin fetur. Kungiyar IPMAN ya ce za ta sayar da litar fetur a farashin Dangote. An sa ranar fara ganin ragin.

NNPC ya ce tsohuwar matatar Fatakwal na aiki, tana samar da man fetur da dizel, bayan gyaran dala biliyan 1.5; kamfanin ya roki jama'a su daina yarda da jita jita.

Matatar Dangote ta nemi NNPCL ta rika fadin labari yadda ya ya ke. Matatar na martani ne kan cewa ta ranci Dala biliyan daya domin ta fara gudanar da aiki.

NNPCL ya karbi bashin dala biliyan 1 don tallafawa matatar man Dangote, ya kuma jagoranci sake bude matatar Fatakwal da samun riba a karkashin Kyari.
Yan jihohi masu arzikin man fetur
Samu kari