Rikcin makiyaya a Najeriya
Gwamnatin jihar Gombe ta dakatar da sarakunan gargajiya kan manoma da makiyaya a karamar hukumar Funakaye. Rikicin ya yi sanadiyar mutuwar mutane.
Wani rikici da ya barke tsakanin manoma da makiyaya a jihar Benue ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 3. Har yanzu ana neman mutum daya da ba a same shi ba.
Rikicin manoma da makiyaya ya yi kamari a karamar hukumar Darazo da ke jihar Bauchi ya jawo daina zuwa gona. Manoma sun bukaci gwamna ya dauki mataki.
Ana fargabar makiyaya sun kashe mutane 9 ciki har da dan sanda a Benue, yayin da matsalar tituna ke hana jami’an tsaro isa cikin gaggawa domin ceto rayuka.
Sabon rikici ya barke a jihar Filato tsakanin makiyaya 'yan kabilar Fulani da wasu mazauna karamar hukumar Bokkos. An kashe wata mata tare da kona gidaje.
'Yan ta'adda da ake zargin Fulani makiyaya ne sun kone gidaje 100 a yankin Bandawa Gwenzu na karamar hukumar Karim Lamido a Taraba. Mutum 1 ya mutu.
An shuga jimami bayan barkewar wani rikici a tsakanin manoma da makiyaya a jihar Neja. Rikicin ya jawo an samu asarar rai yayin da aka raunata wasu da dama.
Makiyaya dauke da miyagun makamai sun harbe Fr. Atongu a hanyar Makurdi–Naka, sun sace mutum 2. An garzaya da shi asibiti domin likitoci su ceto rayuwarsa.
Rikici tsakanin maharba da makiyaya ya jikkata Fulani tara a Bali, Taraba. Lamarin ya samo asali ne daga gardama kan shayar da dabbobi ruwa a rijiyar garin.
Rikcin makiyaya a Najeriya
Samu kari