Hare-haren makiyaya a Najeriya
An samu tashin hankali bayan barkewar fadan Fulani da Manoma a jihar Jigawa. Mutane sun riga mu gidan gaskiya yayin da aka raunata wasu mutum hudu.
Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya sake bude kasuwar dabbobi ta Kara da ke a Birnin Gwari bayan shekaru 10 tana rufe. Ya ce za a mayar da wuta da sadarwa a yankin.
Rikici ya barke tsakanin makiyaya da manoma a yankin Dogon Duste da ke jihar Nasarawa. Rundunar 'yan sanda ta ce mutane uku sun mutu a wannan rikici.
Mutane karamar hukumar Etsako ta Gabas a jihar Edo sun ce kullum yan bindiga sai sun kashe mutane a garin. Yan bindiga na kashe mutane kamar dabbobi a yankin.
An shiga fargaba bayan kisan mutane da dama yayin da rikici ya balle tsakanin manoma da makiyaya a jihar Adamawa, inda jama'a da dama su ka rasa rayukansu.
Ministan tsaro, Mohammed Badaru ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na kokarin kawo karshen rikicin manoma da makiyaya a jihar Plateau da ke yankin Arewa ta Tsakiya.
Wasu da ake zargin makiyaya ne sun kashe sojoji biyu da farar hula bakwai, ciki har da hakimin kauyen Eguma da ke karamar hukumar Agatu ta jihar Benue.
A labarin nan, kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah Cattle Breeders Association (MACBAN), ta bayyana matakin da ta dauka wajen rage rikicin manoma da makiyaya.
Ana fargabar an kashe mutum daya yayin da fada ya kaure tsakanin makiyaya da manoma a kauyen kauyen Barkta da ke cikin karamar hukumar Bosso ta jihar Neja.
Hare-haren makiyaya a Najeriya
Samu kari