Hare-haren makiyaya a Najeriya
rundunar 'yan sanda ta kama wani mutum da ya rika yada takarda cewa Fulani makiyaya za su kai hari Imo. Ya ce Allah ya yi wahayi ne ga malamar coci.
Jihar Jigawa da ke fama da matsanancin rikicin manoma da makiyaya ta fara kokarin hada kan bangarorin biyu domin tabbatar da an daina zubar da jinin jama'a.
Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed ya kafa ma'aikatar kiwo domin magance matsala da rikicin manoma da makiyaya da bunkasa tattalin jihar a Itas Gadau.
An samu tashin hankali bayan barkewar fadan Fulani da Manoma a jihar Jigawa. Mutane sun riga mu gidan gaskiya yayin da aka raunata wasu mutum hudu.
Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya sake bude kasuwar dabbobi ta Kara da ke a Birnin Gwari bayan shekaru 10 tana rufe. Ya ce za a mayar da wuta da sadarwa a yankin.
Rikici ya barke tsakanin makiyaya da manoma a yankin Dogon Duste da ke jihar Nasarawa. Rundunar 'yan sanda ta ce mutane uku sun mutu a wannan rikici.
Mutane karamar hukumar Etsako ta Gabas a jihar Edo sun ce kullum yan bindiga sai sun kashe mutane a garin. Yan bindiga na kashe mutane kamar dabbobi a yankin.
An shiga fargaba bayan kisan mutane da dama yayin da rikici ya balle tsakanin manoma da makiyaya a jihar Adamawa, inda jama'a da dama su ka rasa rayukansu.
Ministan tsaro, Mohammed Badaru ya bayyana cewa gwamnatin tarayya na kokarin kawo karshen rikicin manoma da makiyaya a jihar Plateau da ke yankin Arewa ta Tsakiya.
Hare-haren makiyaya a Najeriya
Samu kari