Fulani Makiyaya
'Yan bindiga sun hallaka shugaban matasa na kungiyar Miyetti Allah a jihar Plateau mai suna Yakubu Muhammad a daren jiya Alhamis 18 ga watan Yulin 2024.
Batun haramta kiwon sake ga dabbobin makiyaya na yamutsa hazo tsakanin masu ruwa da tsaki a Najeriya, inda kungiyoyin makiyaya ke ganin zai jawo rashin zaman lafiya.
Hukumar kula da zirga zirgar jiragen kasa a Najeriya (NRC) ta sanar da cewa nan da watanni kadan za a cigaba da jigilar shanu daga Arewa zuwa Kudu a jirgin kasa.
Shugaba Bola Tinubu ya kirkiro ma'aikatar raya dabbobi. An sanar da kirkirar ma’aikatar ne a yayin kaddamar da kwamitin aiwatar da gyara kan harkokin kiwon dabbobi.
Wasu makiyaya sun gwabza fada da jami'an tsaro na rundunar Amotekun a jihar Ondo. Makiyayan sun farmaki jami'an tsaron ne kan hana su yin barna a gonaki.
Rundunar 'yan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar wasu mutum biyu sakamakon barkewar rikici a tsakanin manoma da makiyaya ranar Talata a jihar.
ahotanni sun ce 'yan ta'adda sun kai hari kauyen Rugar Sojidi da Fulani ke zaune a kusa da Issan Makaranta da ke karamar hukumar Kagarko a Kaduna.
Kungiyar Fulani makiyaya ta (MACBAN) ta bukaci a kare martaba da kimar kujerar Sarkin Musulmi, Alhaji Sa'ad Abubakar III. Ta gargadi gwamnatin Sokoto.
Rikicin manoma da makiyaya a jihar Jigawa ya yi jawo asarar rayukan mutane uku a yankin gandun dajin Baranda da ke karamar hukumar Kiyawa, har an ceto wasu.
Fulani Makiyaya
Samu kari