Wahalar man fetur a Najeriya
Manyan dilolin mai, Ardova Plc da MRS Oil Nigeria Plc, waɗanda dukkansu abokan huldar matatar Dangote ne, sun rage farashin fetur zuwa N865 a gidaje man su.
PENGASSAN ta zargi dillalan fetur da tsadar mai, duk da faduwar farashin danyen mai a duniya. Kungiyar ta ce ya kamata fetur ya koma N700 zuwa N750.
Yayin da ake ta bikin babbar sallah a Najeriya, yan kasuwar man fetur sun rage farashin litar mai don jawo hankalin masu saya da ƙara gasa a kasuwa.
Najeriya ta shiga cikin ƙasashe 10 mafi arhar man fetur a Afirka, yayin da Libya da Angola ke a kan gaba, duk da matsalolin makamashi da karancin tallafi.
Yayin da ake fama da matsaloli daban-daban game da hakar man Kolmani a bakin iyakar Gombe da Bauchi, gwamnatocin jihohin 2 sun gana da wakilan NNPCL.
Duk da saukar farashi daga Dangote zuwa N875-N905, gidajen mai na sayar da man fetur a kan N890-N910, yayin da suke kukan asara saboda rage kudin da Dangote ke yi.
Dangote ya rage farashin fetur zuwa ₦825, inda gidajen mai na abokan hulɗarsa ke saida lita tsakanin ₦875 zuwa ₦905, ya danganta da yankin da mutane suke.
Rahotanni sun bayyana cewa wani abu ya fashe a sashen gas na wani gidan mai a Fatakwal, babban birnin jihar Ribas, mutum biyar sun ji raunuka, motoci sun ƙone.
Kamfanin Dangote ya sake rage farashin man fetur zuwa N825, daga 835 a matatar mansa da ke Legas don bai wa 'yan Najeriya damar sayen fetur din a farashi mai sauƙi.
Wahalar man fetur a Najeriya
Samu kari