Yaki da ta'addanci a Najeriya
Malamin Musulunci, Sheikh Ahmad Abubakar Gumi ya yi magana kan zuwan sojojin Turkiyya Najeriya, inda ya ce yana maraba da su domin magance rashin tsaro.
A labarin nan, za a ji cewa jam'iyyar ADC da ke hamayya da gwamnatin tarayya ta ce akwai babbar matsala a shirin dawo da ƴan ta'adda cikin jama'a.
Gwamnatocin Najeriya da Turkiyya za su kafa cibiyar horas da sojoji a Najeriya domin taimakon kasar ta magance matsalar tsaro da ta yi katutu a Najeriya.
Ana zargin cewa 'yan ta'addar Boko Haram sun kashe sojoji 4 da farar hula 1 a garin Mussa, Borno a ranar 15 ga Afrilu, 2026, yayin da sojoji suka dakile harin.
Rundunar sojojin Najeriya ta gudanar da jana'izar Janar da dakarunta da suka rasa rayukansu a hannun tsagerun 'yan ta'addan Boko Haram a jihar Borno.
Bincike ya nuna iƙirarin sojojin Amurka sun kama ƴan Najeriya 8 masu tallafa wa ta’addanci ƙarya ne. An gano Amurka ta sanya takunkumi kan mutane 8 ne kawai.
Peter Obi ya lashi takobin yaƙar ƴan ta'adda ba tare da wata kafar sulhu ba ma damar ya zama shugaba kasa, tare da neman haɗin gwiwar El-Rufai da Kwankwaso.
Sanata Ali Ndume ya bayyana cewa Najeriya na da ikon kawo ƙarshen matsalar tsaro cikin watanni shida idan gwamnatin tarayya ta nuna ƙwazo da jajircewa.
Tubabben dan bindiga, Wada Yellow Musaya ya bayyana cewa wasu yan ta'adda da suka shigo Katsina daga Zamfara ne suke kai sababbin hare-hare har a kan iyalinsa.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari