Yaki da ta'addanci a Najeriya
Sojoji sun hallaka 'yan bindiga 23 ta hanyar harin sama a jihar Katsina bayan sun tsere daga Kano; an lalata makamai da babura yayin da aka dawo da zaman lafiya yau.
Tsohon ɗan Majalisar Dokokin Jihar Ogun, Hon. Musa Moruf, ya samu ’yanci bayan kwana uku a hannun masu garkuwa da mutane bayan sace shi a masallaci.
Jirgin yaki marar matuƙi na Rundunar Sojojin Saman ya faɗi a dajin Zangata da ke karamar hukumar Kontagora da ke Jihar Niger, bayan rasa sadarwa.
Gwamnan Katsina, Dikko Radda, ya ce zaman lafiya na dawowa a wasu kananan hukumomi da ‘yan bindiga suka addaba, yana sa ran 2026 za ta fi armashi.
EFCC ta gurfanar da kwamishinan Bauchi kan zargin tallafa wa ta’addanci da dalar Amurka $9.7m; an tura shi gidan yarin Kuje yayin da yake jiran hukuncin beli.
Babbar hedkwatar sojojin Najeriya ta jaddada cewa an samu nasara a farmakin da Amurka ta kai jihar Sakkwato, ta ce za a fitar da cikakkun bayanai nan gaba.
Gwamnatin Jwara ta gargadi jama'a da su kula kuma su sanya ido yayin ibadar cikar shekara da bukukuwan sabuwar shekara, ta ce yan bindiga na kulla makirci.
Sojojin Najeriya sun hallaka ɗan ta’adda a Bama, sun ruguza sansanoninsu a Sambisa, sannan sun ƙwace jirgi marar matuki na ISWAP a yankin Izge da ke jihar Borno.
Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya musanta zargin ta’addanci, yana cewa bai da alaƙa da ‘yan ta’adda kuma bai taɓa goyon bayan aikata laifi ba.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari