
Yaki da ta'addanci a Najeriya







Majalisar dattawa ya bayyana takaicin yadda ake ci gaba da samun matsalolin tsaro a sassan kasar nan, wanda ya sa ta gayyaci shugabannin tsaro su bayyana a gabanta.

Rundunar 'yan sandan kasar nan ta yi nasarar hallaka matashin dan ta'adda, Dogo Saleh, wanda aka hakikance ya jawo asarar rayukan jama'a da dama bayan garkuwa da su.

Rahotanni sun bayyana cewa jami'an tsaron da ke cikin ayarin Gwamna Babagana Umaru Zulum sun fatattaki ƴan Boko Haram da suka tare matafiya a Borno.

‘Yan ta’addar Lakurawa sun kashe mutum 13 a Birnin Dede, Kebbi, sun kona kauyuka 7, a ramuwar gayya bayan kisan shugabansu Maigemu da dakarun tsaro suka yi.

Matan Jato Aka sun bukaci gwamnati ta dakatar da kashe-kashe, ta kara tsaro, tare da kawo agajin gaggawa ga 'yan gudun hijira da rikici ya raba da gidajensu.

Mayakan kungiyar 'yan ta'addan ISWAP sun kai farmaki a kan wani sasanin Fulani makiyaya dake jihar Borno, amma an samu daukin sojoji kafin lamarin ya kazanta.

An fi fada tsakanin 'yan banga da 'yan bindiga a jihar Zamfara. An kashe mutane 12 cikin 'yan banga yayin da aka gaza gano adadin 'yan bindiga da aka kashe.

Gwamnatin Najeriya ta ayyana Simon Ekpa da wasu mutum 15 a matsayin masu daukar nauyin ta’addanci tare da bukatar a rufe kadarorin da ke da alaka da su nan take.

Har yanzu Boko Haram ta ki sakin iyalan alkalin babbar kotun jihar Borno da aka sace tun a watan Yuni na shekarar 2024 saboda gaza biyansu fansar $500,000.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari