Yaki da ta'addanci a Najeriya
Shugaban hukumar DSS, Oluwatosin Ajayi ya bada umarnin sakin mutane uku da aka kama bisa zargin ta’addanci, bayan binciken hukumar ya tabbatar da ba su da laifi.
Kungiyar kwadagon NLC za ta yi zanga zanga a ranar 17 ga Disambar 2025 a dukkan jihohin Najeriya da Abuja. Za a yi zanga zangar ne saboda sace dalibai a jihohi.
Ministan Tsaro Bello Matawalle ya kai ƙara kotu domin dakatar da kafofin yaɗa labarai daga wallafa rahotannin da ke zarginsa da alaƙa da ’yan ta’adda.
Gwamnatin tarayya ta shaida wa tawagar Amurka da ta kawo ziyara Najeriya cewamatsalar tsaron da ta addabi kasar nan ba ta da alaka da tauye wani addini.
Rundunar 'yan sanda ta tabbatar da kama wanda ya jagoranci garkuwa da dan Majalisar dokokin Anambra, Justice Azuka tare da kashe shi a shekarar 2024 da ta gabata.
Kasar Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro na shekaru biyar domin karfafa hadin gwiwa ta horo, leken asiri, kera makamai a tsakaninsu.
Sabon kwamandan Operation Fansan Yamma, Manjo Janar Warrah Idris ya gana da gwamna Dauda Lawal a Zamfara. Ya ce za su kawo karshen 'yan bindiga a Zamfara.
A labarin nan, za a ji cewa rundunar tsaron ƙasar nan ta samu nasarar raba wani mugun jagoran ɗan ta'adda da duniya. An kashe Kalamu a sumanen da aka kai jihar.
Rundunar 'yan sandan Najeriya a jihar Ondo ta sanar da cewa ta kama wani mai garkuwa da mutane yayin da ya ke shirin cire kudin fansa a wani shagon POS.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari