Gwamnatin tarayyar Najeriya
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da karin wa'adin watanni shida ga babban kwanturola janar na hukumar Kwastam ta Najeriya, Adewale Adeniyi.
Gwamnatin tarayya ta bukaci yan Najeriya du rika bai wa nassrorin jami'an tsaro muhimmanci wajen yada labaransu, su kuma daina saka ayyukan yan bindiga a sahun gaba.
Gamayyar jam'iyyun siyasa a Najeriya ta goyi bayan kiran da yan Majalisar wakilai na tsagin adawa suka yi ga Shugaba Bola Tinubu kan matsalolin kasar nan.
Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ƙaddamar da rabon buhunan taki sama da 515,000 ga manoma 128,930 domin ƙara yawan amfanin gona da tsaron abinci.
Kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) ta karbi bayanai tare da amince wa da kudirin kafa rundunar yan sandan jihohi yayin da tsaro ke kara tabarbarewa.
Yan majalisar wakilan tarayya na jam'iyyun adawa sun bukaci shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci kasar nan yadda ya kamata ko ya yi murabus.
Gwamnatin tarayya ta ware kimanin N50m domin tallafa wa masu fama da cutar daji, inda za a ba kowane wanda ya cancanta akalla tallafin Naira 100,000.
Ma'aikatar kudi ta tarayya ta musanta labarin cewa gwamnatin Tinubu na shirin dora karin haraji a harkokin sadarwa da man fetur, ta ce labarin ba gaskiya ba ne.
Kungiyoyin NLC da TUC sun sanar da shirin fara tattaunawa da gwamnatin tarayya kan sabon mafi karancin albashi, saboda hauhawar farashi da ta yi wa ma’aikata katutu.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari