Ma'aikatar Ilimin Najeriya
Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta bayyana cewa ta gano dubannan matasan kasar nan da ke karyar sun kammala manyan makarantu.
Ministan Ilimi a Najeriya, Farfesa Tahir Mamman ya bukaci kungiyoyi masu zaman kansu su yi koyi da Dakta Emeka Offor wajen tallafawa harkar ilimi a Najeriya.
Kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), ta ce a yanzu dai ta dakatar da batun shiga yakin aiki zuwa wani dan lokaci domin tattaunawa da masu ruwa da tsaki.
Gwamnatin tarayya ta dauki gabarar magance gurbata yanayi da ake yi da robobi da leda ta hanyar haramta amfani da su sau daya kawai a ma’aikatu da hukumoni.
Gwamnatin Kano ta zargi tsohuwar gwamnatin da gazawa wajen inganta ilimi bayan ta samu dalibai miliyan 4.7 na zama a kasa babu kujeru a makarantunsu.
Hukumar da ke lura da asusun bayar da lamunin karatu na kasa (NELFUND) ta tabbatarwa ‘yan Najeriya cewa za ta bawa daliban da su ka dace lamunin karatun.
Gwamna Abba Kabir Yusuf zai gina dakunan bincike 300 da samar da malamai 10,000 domin inganta ilimi a jihar. Hakan ya biyo bayan dokar ta baci ga ya saka ne.
Gwamnatin jihar Kano ta amince da fitar da naira biliyan 2,910,682,780 domin biyan kudin jarabawar NECO da NBAIS ga dalibai 119,903 da ba sa iya biyan kudin.
Kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja ya zayyana sunayen wa wasu hukumomi da ma’aikatun gwamnati da zai katse wutar su saboda rashin biyan kudin wutar.
Ma'aikatar Ilimin Najeriya
Samu kari