Yan bindiga
Wani dan bindiga ya kashe mutum daya tare da jikkata akalla mutum 10 a wani hari da ya kai jihar Texas a Amurka. Ya shafe sa'o'i yana fito na fito da 'yan sanda.
Shugaban kasar Najeriya, Bola Tinubu ya gargadi 'yan bindiga da masu daukar nauyin ta'addanci su mika wuya ko su fuskanci karfin gwamnati ba tare da jin kai ba.
Jami'an tsaro a jihar Kogi sun tabbatar da mutuwar fitaccen ɗan bindiga da akae kira Ibrahim Baccujo bayan an dakile yunkurin sace ɗaliban WAEC a Iluke.
Gwamnan jihar Katsina, Dr. Dikko Umaru Radda, ya bukaci 'yan bindiga da ke addabar mutane da su zabi hanyar ci gaba maimakon barna domin su rayu.
Majalisar Dattawa a Najeriya ta umarci hukumomin tsaro da na leken asiri su gano tare da cafke 'yan bindiga da 'yan ta'adda masu nuna kudade a TikTok.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin da ya jawo sanadiyyar kashe 'yan sa-kai a jihar Plateau. Mutanen yankin sun shiga alhini da fargabar kisan.
Wata kungiyar Musulmi ta FASON ta bayyana cewa addinin Musulunci ba shi da alaka da ta'addanci, garkuwa da mutane, fashi ko sauran miyagun laifuka.
Wata mota dauke da fasinjoji ta taka wani bam da ake zargin 'yan bindiga ne suka dasa shi a jihar Zamfara. Mutane sun rasu yayin da wasu suka jikkata.
Jami'an rundunar 'yan sandan babban birnin tarayya Abuja, sun samu nasarar bindige wasu 'yan bindiga. Sun kuma ceto wasu mutane da suka yi garkuwa da su.
Yan bindiga
Samu kari