Yan bindiga
Kakakin rundunar sojojin Safe Heaven, a jihar Filato, Samson Zhakom ya ce sojojin rundunar sun cafke 'yan bindiga da masu kai masu makamai a Filato da Kaduna.
Yan bindiga sun kai hari kan matafiya a hanyar Sokoto zuwa Kaduna inda suka kashe Farfesa Yusuf Saidu na jami'ar Usman Danfodiyo. Jami'ar ce ta sanar da haka.
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar, ya yi magana kan matsalar rashin tsaron da ta addabi yankin Arewa maso Yamma na Najeriya.
Jami'an tsaro sun samu nasarar cafke wata mata mai safarar makamai ga 'yan ta'adda a jihar Katsina. An cafke ta ne dauke da alburusai a cikin jaka.
Rundunar ‘yan sanda ta cafke wasu mutane hudu da ake zargi da kashe wani Birgediya Janar Uwem Udokwere mai ritaya a gidansa da ke Abuja a ranar Asabar.
Tsohon dan takarar gwamna a jam'iyyar AFGA, Dakta Abdullahi Sani Shinkafi ya soki gwamna Dauda Lawal Dare kan kashe N62.8b kan gina filin jirgin saman Gusau.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun yi awon gaba da wani jami'in 'yan sanda da direban wani babban basarake a jihar Rivers bayan sun kai farmaki a fadarsa.
Rundunar ƴan sanda a jihar Katsina ta tabbatar da mutuwar mutane bakwai a harin da ƴan bindiga suka kai a karamar hukumar Danmusa da ke jihar a jiya Asabar.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun shiga har cikin gida sun sace wani babban limamin cocin Katolika a jihar Zamfara. 'Yan sanda sun fara kokarin kubutar da shi.
Yan bindiga
Samu kari