Jihar Edo
Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya bayyana cewa za a yanke hukuncin kisa ga duk wani mai garkuwa da mutane da aka samu da aikata laifin a jihar.
Bayan kisan kiyashin da aka yi wa Hausawa a Edo, dan majalisar tarayya, Kabiru Rurum, ya shawarci jama’arsa su daina farauta a Kudu saboda matsalolin tsaro.
Jam’iyyar PDP ta sake samun matsala a jihar Edo bayan dan majalisar dokoki, Nicholas Asonsere ya sauya sheka zuwa jam'iyyar APC mai mulkin jihar.
Rundunar ‘yan sanda a Edo ta ce an cafke mafarauta hudu daga Kano da makamai yayin da suka isa jihar ranar Asabar da dare a dakin hotel da ke jihar.
Bayan dawowa daga Edo, mataimakin gwamnan Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya tabbatar da cewa yan Arewa da ke zaune a Edo suna cikin aminci da kwanciyar hankali.
Gwamnan jihar Edo ta bayyana cewa an kafa kwamiti na musamman domin gano musabbabin kisan Hausawa 16 a Edo bayan mataimakin gwamnan Kano ya isa Edo.
Gwamna Monday Okpebholo ya ce gwamnatinsa da ta tarayya sun kafa kwamitin bincike don gano musabbabin kisan matafiya 16 'yan Kano a Uromi, jihar Edo.
Bayan kisan Hausawa 16 a Edo, gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa jihar da ya haɗa mataimakin gwamna domin binciken kashe-kashen da suka faru a kauyen Uromi.
Shugaban kwamitin majalisa mai kula da rundunar sojin kasa ya ce dole a saka ido a kan 'yan banga da basu horo na musamman bayan kisan Hausawa da aka yi a Edo.
Jihar Edo
Samu kari