Matsin tattalin arziki
Tun bayan sanar da ƙarin kudin kira da kaso 50% da NCC ta yi, an samu manyan ƙungiyoyi da suka fara fito-na-fito da gwamnatin Bola Tinubu kan wannan mataki.
Babban Bankin Najeriya (CB) ya yi alkawarin ci gaba da aiwatar da manufofin kare tattali a 2025 yayin da ya kare hauhawar farashin kaya a cikin ƙasar nan a 2024.
Hukumar FIRS ta ce ta tatso kudin shigar Naira Tiriliyan 21.6 ta haraji a 2023. Hakazalika, hukumar ta shaida cewa tana son tara Naira tiriliyan 25 a 2025.
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umar Finitiri ya caccaki tsarin da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta dora tattalin arzikin Najeriya, inda ya ke ganin dole a gyara.
Rahotanni sun ce Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ƙaddamar da wasu matakai don karfafa darajar Naira, ciki har da sassauta wasu dokoki ga ‘yan kasuwar canji.
Rundunar 'yan sandan Kano ta bayyana cewa za ta saka kafar wando daya da duk wani jami'inta da aka gano ya na karbar na goro a titunan da ke fadin jihar.
Kungiyar kwadago ta Najeriya (NLC) ta bayyana shirinta na yin zanga-zanga a ranar Talata, 4 ga watan Fabrairu, 2025 kan ƙarin kudin kiran waya da data.
Gwamnatin Jigawa ta ware Naira biliyan 4.8 don ciyar da mabukata 189,000 a Ramadan. Haka kuma, za a gyara asibitoci 114, wanda zai ci Naira biliyan 9.7.
Yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan raba awaki, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kare shirin yana cewa naman awaki na da amfani sosai wajen magance cututtuka.
Matsin tattalin arziki
Samu kari