Kasar waje
Dakarun sojojin kasar Denmark sun shirya da makamai domin tunkarar sojojin Amurka kan yunkurin mamaye tsibirin Greenland da Donald Trump ko son yi.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa yana nazarin rage yawan sojoji a Gabas ta Tsakiya sakamakon yakin da ya ke da Iran. Tehran ta ki yarda da batun.
Wani dan jarida mai zaman kansa a kasar Amurka, Nathan Levins ya yi ikirarin cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya rasu. Ya ce an yi zaman makoki.
Gwamnatin Amurka ta tura dakarun soji na musamman (MEU) guda 2,500 tare da wasu sojoji da jiragen yaki zuwa Gabas ta Tsakiya, inda za su yi yaki da Iran.
Switzerland ta tabbatar da cewa ta yi watsi da buƙatun Amurka na amfani da sararin samaniyarta don kai hari Iran, kuma ta soke kasuwancin makamai da kasar.
Ma’aikatar harkokin wajen Rasha ta gayyaci jakadan Isra’ila Oded Joseph domin bayani kan harin da ya jikkata ‘yan jaridar RT a Lebanon wanda ya jawo magana.
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya jawo ce-ce-ku-ce kan kalamansa da suka shafi Annabi Isa da Genghis Khan, yayin da ya musanta nuna ƙiyayya ga Kiristoci.
Jagoran kasar Iran, Mojtaba Khamenei ya sanar da cewa za a cika azumi 30 gobe Juma'a, sannan za a yi sallah karama ranar Asabar, 21 ga watan Maris, 2026.
Hukumar leken asirin Amurka ta mika rahoto kan shirin nukiliyar Iran ga Majalisar Dattawan Amurka, ta ce har yanzu jamhuriyar Musulunci ba ta sake gina su ba.
Kasar waje
Samu kari