Kasar waje
Rundunar sojin Israel ta ba da umarnin kwashe garuruwa 11 a kudancin Labanon yayin da take tsananta hare-hare, lamarin da ke barazanar haifar da sabon gudun hijira.
Wani babban jami'i a rundunar sojin Iran ya tabbatar da cewa har yanzu akwai yiwuwar jamhuriyar ta Musulunci ta sake komawa fagen fama da Amurka.
Ministan harkokin wajen Faransa ya zargi Isra'ila da muzgunawa Kiristoci a Jerussalem da wasu wurare. Ya ce ba za su zuba ido game da lamarin ba sam.
Halin da ake ciki na rikici tsakanin Amurka, Isra'ila, da Iran ya riga ya fara yin tasiri ga yanayin kuɗaɗen mutane a ƙasar Ingila ta fannoni daban-daban.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sake mika kudirin zaman tattaunawa tsakaninta da Amurka, a wani yunkuri na kawo karshen yakin da kasashen suka yi gaba daya.
Kamfanin Mercedes-Benz ya kai ƙarar Victor Osimhen gaban ƴan sandan Italiya kan zargin gazawa wajen biyan bashin €90,000 na motar da ya yi hayarta tun 2023.
A labarin nan, za a ji abubuwan da ƙasashen Rasha da Amurka suka tattauna bayan doguwar gana wa ta kusan mintuna 90 tsakanin Vladimir Putin da Trump.
Shugaban ƙasar Kenya, William Ruto, ya bayyana cewa an karkatar da maganganunsa kan Turancin ’yan Najeriya, yana cewa an faɗe su ne a tattaunawar sirri.
Wakilan gwamnatin Jamus sun gana da Musulmi da Kirista a Najeriya kan matsalar tsaro. Thomas Rachel ya ziyarci wuraren da aka kai hari a jihar Benue.
Kasar waje
Samu kari