Kasar waje
Gwamnatin Najeriya ta hada kai da Faransa domin inganta tattara haraji. Sababbin dokokin harajin Najeriya na Bola Tinubu za su fara aiki a farkon 2026.
Sojojin Amurka sun kwace wani jirgin kaya da ya fito daga China zai tafi kasar Iran. Sojojin sun cire wasu kaya a jirgin a kusa da tekun Sri Lanka a Nuwamban 2025
Kasar Benin da fara dawowa cikin kwanciyar hankali bayan dakile yunkurin juyin mulki a fadin kasar. Mutane sun fara komawa bakin aiki yayin da aka bude makarantu.
Ministan Tsaro, Christopher Musa ya yaba da saurin daukar matakin sojojin Najeriya wurin dakile juyin mulkin Benin da aka yi yunkurin yi a karshen mako.
Wani jami'in gwamnatin Benin ya bayyana cewa sun gano inda sojan da ya jagoranci yunkurin juyin mulki a kasar, Benin ya fake a kasar Togo. Za su nemi maido shi.
An yi ambaliyar ruwa a kasar Saudiyya inda mutane 12 suka rasu, an ceto mutane 271 tare da tattara mutane 137 da suka rasa gidajensu a kasar Saudiyya.
Gwamnatin Najeriya ta fara tattaunawa da gwamnatin Burkina Faso karkashin Ibrahim Traoré game da jirgin sojojin saman Najeriya da Burkina Faso ta tsare.
Tsohon hafsan sojoji, Tukur Buratai ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu kan saurin dakile yunkurin juyin mulki a Benin, ya kira matakin “gagarumin dabara”.
Gwamnatin Faransa ta ce ta taimaka wa kasar Benin dakile sojojin da suka nemi kifar ga gwamnatin shugaba Patrice Talon a ranar Lahadi. Najeriya ma ta kai dauki.
Kasar waje
Samu kari