Kasar waje
Sojoji sun bayyana a gidan talabijin na Benin inda suka sanar da rushe gwamnati, alamu na juyin mulki da ya kifar da Patrice Talon wanda ya shafe shekaru a mulki.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya karyata rade-radin kama shi a Faransa, yana mai cewa duk ƙagaggun labarai ne da nufin neman karkatar da hankalinsa daga aikinsa.
'Yan bindiga dauke da miyagun makamai sun kai hari inda ake aikin gina titin Saadu-Kaiama-Kosubosu a karamar hukumar Ekiti, jihar Kwara, inda aka sace 'yan China 2.
Tsohon Firayim Ministan Biritaniya, Boris Johnson, ya ce ya ji cikakkiyar tsaro a Owerri duk da rahotannin tsaro da suka gabace shi kafin zuwansa Imo.
Wasu yan sa kai a Katsina sun kai harin kuskure kan sojojin Nijar da suka shiga Mazanya don ɗibar ruwa, lamarin da ya jawo damuwa har hedikwatar tsaro ta shiga ciki.
Daya daga cikin jagororin 'yan adawa a kasar Kamaru, Anicent Ekane ya rasu a hannun sojoji kwanaki bayan Paul Biya ya kama shi saboda wasu zarge-zarge.
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya gana da Bola Tinubu a fadar shugaban kasa kan rikicin siyasar da ta barke bayan juyin mulki a Guinea-Bissau.
Tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan ya ce ya ce juyin mulkin Guinea Bissau ya fi masa zafi a kan kayar da shi zabe da Buhari ya yi a 2015.
Tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan, ya bar Guinea-Bissau lafiya bayan rikicin siyasa, inda Ma’aikatar Harkokin Waje ta tabbatar da cewa babu wata matsala.
Kasar waje
Samu kari