Jam'iyyar APC
Jigo a jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya, Stanley Osifo, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027. Zai fafata da Shugaba Bola Tinubu.
Gwamna Babajide Sanwo -Olu na jihar Legas ya bayyana goyon bayansa ga mataimakinsa, Kadri Hamzat a matsayin wanda zai gaje shi a zaben 2027 mai zuwa.
Gwamnan jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, zai fafata da dan kasuwb da ya shigo siyasa, Abdulrahaman Chakwam, domin samun tikitin takarar sanata a 2027.
A labarin nan, za a ji matasan Borno sun bayyana dalilansu na tara kuɗi domin ya sake neman takarar Sanata a karo na biyar yayin da shekarar 2027 ke kara karatowa.
Tsohon kwamishina a Zamfara, Sheikh Abdullahi Maharazu Mafara ya gamu da tsautsayi bayan ‘yan bindiga sun bude masa wuta a hanyar zuwa taron APC.
Farfesa Mohammed Sani Haruna ya ce ba zai janye takararsa ba duk da goyon bayan gwamna ga Sanata Aliyu Wadada, yana shirin fafatawa a zaben fidda gwani na APC.
Gwamnonin Arewacin Najeriya guda 10 ne ke neman tazarce a zaben shekarar 2027 bayan nasarar farko a zaben 2023 da aka yi a fadin kasar baki daya.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum ya nemi afuwar jiga-jigan APC kan mulkinsa na shekaru bakwai, an ga yana zubar da hawaye a wurin taro a Maoduguri.
Jam’iyyar APC a Kebbi ta shirya gagarumin gangamin hadin kai na mutum miliyan daya domin nuna goyon baya ga Bola Tinubu da Gwamna Nasir Idris a zaben 2027.
Jam'iyyar APC
Samu kari