Jam'iyyar APC
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya aika da sako ga mambobin jam'iyyar APC kan zaben fitar da gwani. Shugaba Bola Tinubu ya bukaci su hada kawunansu.
Tsohon gwamnan jihar Ondo, Olusegun Mimiko, ya sauya sheka zuwa jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya. Olusegun Mimiko ya nuna goyon bayansa ga Bola Tinubu.
Tsohon shugaban rundunar 'yan sandan Najeriya, Usman Alkali Baba, ya janye daga neman takarar gwamnan jihar Yobe a karkashin inuwar jam'iyyar APC.
Masu neman takara a karkashin jam'iyyar APC a zaben 2027 sun dura ofishin jam'iyyar da gidan shugaban jam'iyyar suna jiran sakamakon tantance su.
Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa Atiku Abubakar da sauran 'yan adawa na taimaka masu. Ya ce yadda suke caccakae juna abin burgewa ne ga APC.
Mai neman takarar gwamna a Taraba a karkashin jam'iyyar APC, David Sabo Kente ya ce dole a yi adalci ko jam'iyyar ta rushe a zaben 2027 da ke tafe.
Tsohon minista a Najeriya, Femi Fani-Kayode ya nuna goyon baya ga Sheikh Isa Ali Pantami yayin da ake shirin zaben fitar da gwani na jam'iyyar APC a Gombe.
Gwamnan Rivers, Siminalayi Fubara, ya musanta rade-radin da ke yawo a kafafen sada zumunta, yana mai jaddada cewa har yanzu cikakken dan jam'iyyar APC ne.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sulhunta mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin da Abdullahi Tijjani Gwarzo kan zaben 2027.
Jam'iyyar APC
Samu kari