Arewa
Wata Kungiyar matasa mai suna 'Concerned Taraba Youth Group' ta bukaci Gwamna Agbu Kefas ya haɗa kai da Bola Tinubu domin samun ayyukan more rayuwa.
Al’ummar wani yanki a jihar Sokoto sun tura roko da neman alfarma ga gwamnatin Bola Tinubu kan matsalar tsaro da ta ki ci ta ki cinyewa domin kare kansu.
Mazauna Kebbe, Sokoto, sun koka kan hare-haren ‘yan bindiga da suka kashe mutane, suka sace sama da 30, suka lalata garuruwa 17, yayin da gwamnati ta yi martani.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya ce burinsa shi ne haɗa kan al’ummar Najeriya, ya kuma tabbatar da cewa gwamnati za ta yi adalci ga dukkan addinai.
Bayan jin cewa Rarara ya samu digirin girmamawa daga jami'ar European-American, Legit Hausa ta zakulo mawaƙan Hausa 5 da suka taɓa samun irin wannan karramawa.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi shekara biyu a kan mulkin Najeriya. Ana ganin wasu 'yan Arewa na iya mara masa baya don yin tazarce a zaben shekarar 2027.
An tabbatar da cewa Sarkin Kirawa, Alhaji Abdulrahman Abubakar, ya tsere zuwa Kamaru bayan Boko Haram sun kona fadarsa a wannan mako da muke ciki a jihar Borno.
Tsohon Wazirin Zazzau, Alhaji Ibrahim Aminu da Dr Nasiru Bashari Aminu suna zargin kalaman Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli sun bata mutuncinsu.
Rashin tsaro da ya hada da hare haren 'yan bindiga ya tilasta rufe makarantu 188 a Arewacin Najeriya. An rufe makarantu a Katsina, Zamfara Neja da Zamfara.
Arewa
Samu kari