Yaki da rashawa a Najeriya
ICPC ta kai samame gidan El-Rufai na Abuja yau 19 ga Fabrairu, 2026. Lauyan sa ya soki matakin a matsayin haramtacce yayin da ake binciken kudin Jihar Kaduna.
El-Rufai ya sake kwana a hannun EFCC yau 18 ga Fabrairu, 2026. Lauyansa na neman beli yayin da hukumar ke shirin neman izinin kotu don tsawaita tsare shi kan ₦432bn.
Nasir El-Rufai ya amince zai kai kansa ofishin ICPC ranar 18 ga Fabrairu, 2026. Hakan ya biyo bayan yunƙurin kama shi da aka yi a filin jirgin Abuja bayan dawowarsa.
Lauyan El-Rufai ya soki jami'an tsaro kan yunkurin kama shi ba bisa ƙa'ida ba a Abuja yau. Ya ce za su bayyana a ofishin EFCC ranar Litinin, 16 ga Fabrairu, 2026.
Ana zargin cewa fasinjoji sun hana jami'an tsaro tafiya da tsohon gwamnan Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai lokacin da ya sauka filin jirgin sama na Abuja.
Alkali Obiora Egwuatu ya janye daga shari’ar tsohon Minista Abubakar Malami kan zargin N212bn a Abuja. Ya bayyana hakan ne a zaman kotu na yau 12 ga Fabrairu, 2026.
Nasir El-Rufai zai dawo Nijeriya nan da sa'o'i 48 domin amsa kiran EFCC a ranar 16 ga Fabrairu, 2026. Ya musanta zargin tserewa zuwa waje don gujewa masu bincike.
Tsohon Akanta Janar na Tarayya, Ahmed Idris ya fara fuskantar wani kalubalen daga hukumar EFCC, an shigar da sababbin tuhume-tuhume shida kansa a kotu.
Hukumar EFCC ta cika hannunta da wani bawan Allah mai suna Gidado Ibrahim a kan zargin hada baki da wata Halimat Adenike Tejusho wajen karyar nemo aiki a NNPCL.
Yaki da rashawa a Najeriya
Samu kari