
Yaki da rashawa a Najeriya







Hukumar EFCC ta ja hankalin al'umma kan cin hanci da rashawa bisa da cin dukiyar mutane bisa zalunci. EFCC ta jawo ayar Kur'ani domin gargadin jama'a.

Dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar korar wasu mayakan ISWAP da su ka yi yunkurin kai hari wani ofishin 'yan sanda da ke Malari a jihar Borno.

Majalisar Shira ta tsige shugaban karamar hukumar, Abdullahi Beli, da mataimakinsa bisa zarge-zargen rashawa. An nada Hon. Wali Adamu a matsayin mukaddashi.

Hukumar EFCC ta gurfanar da tsohon gwamnan Abia, Theodore Orji, da ɗansa, Chinedum Orji, da wasu mutane biyar kan zargin almundahanar N47bn a kotun Abia.

Hukumar PCACC ta ɗamƙe shugaban ƙaramar hukumar Kiru, Abdullahi Mohammed bisa zargin hannu a badaƙalar sayar da filin da aka ware son gina filin ƙwallo.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da mukaddashin shugaban ma'aikatan jihar, Salisu Mustapha kan zargin cire kudi daga albashin ma'aikata ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta bayyana cewa wasu tsofaffin shugabannin hukumar tattara kudin haraji a jihar sun yi sama da fadi da hakkokin jama'a.

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan kwangilolin bogi da suka lakume Naira biliyan 167, inda ta bukaci a gurfanar da 'yan kwangilar don dawo da dukiyar gwamnati.

EFCC ta gurfanar da Farfesa Usman Yusuf bisa laifuffuka biyar da suka hada da wawure kudi da bayar da fifiko ba bisa ka’ida ba. Kotu ta tsare shi a kurkuku.
Yaki da rashawa a Najeriya
Samu kari