
Yaki da rashawa a Najeriya







Hukumar PCACC ta ɗamƙe shugaban ƙaramar hukumar Kiru, Abdullahi Mohammed bisa zargin hannu a badaƙalar sayar da filin da aka ware son gina filin ƙwallo.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya dakatar da mukaddashin shugaban ma'aikatan jihar, Salisu Mustapha kan zargin cire kudi daga albashin ma'aikata ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta bayyana cewa wasu tsofaffin shugabannin hukumar tattara kudin haraji a jihar sun yi sama da fadi da hakkokin jama'a.

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan kwangilolin bogi da suka lakume Naira biliyan 167, inda ta bukaci a gurfanar da 'yan kwangilar don dawo da dukiyar gwamnati.

EFCC ta gurfanar da Farfesa Usman Yusuf bisa laifuffuka biyar da suka hada da wawure kudi da bayar da fifiko ba bisa ka’ida ba. Kotu ta tsare shi a kurkuku.

SERAP ta bukaci Shugaba Tinubu ya binciki batan Naira biliyan 26 daga PTDF da Ma'aikatar Man Fetur a 2021, tare da mayar da kudaden don rage gibin kasafin kudi.

Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya gargadi shugaba Bola Tinubu kan kama mutane saboda siyasa bayan EFCC ta kama Ferfesa Yusuf Usman na hukumar NHIS.

Dakarun hukumar yaki da rashawa watau EFCC sun kai samame gidan tsohon shugaban NHIS, Farfesa Usman Yusuf, sun kama shi a gidansa da ke birnin Abuja.

Kotun Kano ta hana kama Muhuyi Magaji Rimingado, yayin da 'yan sanda suka fayyace cewa ba kama shi suka yi ba, an gayyace shi ne kawai domin bincike.
Yaki da rashawa a Najeriya
Samu kari