
Aikin Hajji







Bayan ware miliyoyi saboda daukar nauyin Musulmi zuwa aikin hajji, wasu 'yan asalin Ebonyi sun bukaci Majalisar Dokokin jihar Ebonyi ta tsige Gwamna Francis Nwifuru.

An yi ta ce-ce-ku-ce bayan gwamnatin jihar Ebonyi ta bukaci shugabannin kananan hukumomi 13 su dauki nauyin akalla Mahajjaci daya don aikin Hajjin 2025.

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta kara wa'adin lokacin biyan kudin Hajjin 2025. Hukumar NAHCON ta bukaci maniyyata da su biya kudadensu a kan lokaci.

Jami'an hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ta'annati da dukiyar kasa (EFCC), sun kai samame a hedkwatar hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) da ke Abuja.

EFCC ta gurfanar da wani Mustapha Mohammed kan damfarar alhazai Naira miliyan 144 da sunan kai su Umrah. Kotun Gombe ta umarci a tsare shi a gidan yari.

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya ba da shawara kan hanyar gudanar da aikin Hajji. Gwamna Radda ya bukaci a rage yawan kwanakin da Alhazai ke yi.

Hukumar kula da alhazai ta jihar Kwara ta ce ranar ƙarshe ta biyan kuɗin Hajjin 2025 ita ce Janairu 31, 2025. An nemi alhazai su gabatar da fasfo kafin Fabrairu 25.

Hukumar NAHCON ta ce maniyyata aikin hajjin 2025 za su samu tallafin $500. Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi ya fadi matsalolin da aka samu a shekarar 2024.

Hukumar jin dadin Alhazai ta kasa (NAHCON), ta sanya lokacin da maniyyata za su kammala biyan kudaden Hajji na shekarar 2025. NAHCON ta ce ba za ta yi kari ba.
Aikin Hajji
Samu kari