Abun Bakin Ciki
Mutane shida sun mutu a wajen cunkoson daukar aikin sojoji a Accra, Ghana. Gwamnati ta dakatar da shirin kuma Shugaba Mahama ya ziyarci wadanda suka ji rauni.
Gwamnatin kasar Turkiyya ta tabbatar da mutuwar duka sojoji 20 da ke cikin jirgin C-130 da ya yi hatsari a kasar Georgia kusa da iyakar Azerbaijan.
Shahararren lauya a Arewacin Najeriya, Abba Hikima ya goyi bayan matashin sojan da ya samu sabani da Ministan Abuja, Nyesom Wike, yana cewa bai aikata laifi ba.
Ministan Muhalli, Malam Balarabe Lawal, ya rasa mahaifiyarsa, Hajiya Dayyabatu Lawal Aliyu, wadda ta rasu a Zariya bayan rashin lafiya mai tsawo.
Rikici ya barke a Badagry, bayan jami’in hukumar shige da fice ya harbi wata mata, lamarin da ya sa wasu fusatattun matasa suka kona shingen bincike hukumar.
Matar tsohon shugaban kasa, Shehu Shagari, wacce ta rage a raye, Hajiya Sururaya riga mu gidan gaskiya bayan fama da jinya tana da shekaru 79 a duniya.
Sanata Muntaru Dandutse ya mika sakon ta'aziyya bisa rasuwar limamin masallacim yan Izala da ke Funtua, Sheikh Goni Imam Sa'id Musa, ya yi addu'ar Allah jikansa.
Wasu ‘yan bindiga sun harbe kansilan jam’iyyar APGA, Nze Ala Kuru Orji, yayin da yake jefa ƙuri’a a mazabar Ezukaka 1, Orumba ta Kudu a jihar Anambra.
Yan bindiga sun kashe mutum 5, sun sace mata 9 a Bargaje, karamar hukumar Isa, jihar Sokoto. Yanzu haka dai yaran rikakken dan ta'adda Bello Turji, ne ake zargi.
Abun Bakin Ciki
Samu kari