Abuja
Tsagin da jam'iyyar ADC da Nafiu Bala ke jagoranta ya bayyana cewa bai kamata jam'iyyar ta fara sayar da fom din neman takara ba. ya bukaci David Mark ya dakata.
Babban rikici ya raba kan Gwamnonin APC (PGF) a ranar 8 ga Mayu, 2026, inda aka samu ɓangarori biyu ƙarƙashin Hope Uzodimma da Dapo Abiodun gabanin zaɓen 2027.
Babbar kotun tarayya ta ba kwamishinan kuɗi na Bauchi, Yakubu Adamu, izinin tafiya Hajjin 2026 da duba lafiyarsa a Saudiyya a ranar 8 ga Mayu, 2026.
Sabon ministan makamashi a Najeriya, Joseph Tegbe ya musanta rahoton cewa ya yi alkawarin gyara matsalar lantarkin Najeriya cikin watanni uku yayin tantance shi.
Tsohon ministan sufuri a Najeriya, Femi Fani-Kayode ya ce shi ne ya nemi a mayar da shi daga Jamus zuwa Afirka ta Kudu saboda ra'ayinsa da kusancin ƙasashen biyu.
Majalisar dattawan Najeriya ta sauya sababbin dokokin da ta bullo da su domin hana wasu sanatoci neman mukamai. Ta ce za su saba da kundin tsarin mulki.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya sake jawo maganganu a Najeriya bayan izgili ga ubangiji kan shirin sake fasalin Jabi da wata Fasto Sarah Omakwu ke rokonsa.
Kotun Abuja ta saka ranar 8 ga Mayu, 2026, domin sauraron ƙarar rikicin shugabancin ADC tsakanin David Mark da Nafiu Gombe, bayan hukuncin Kotun Ƙoli.
Kotun Abuja ta ba da umarnin ƙwace kadarori guda 9 na Timipre Sylva zuwa hannun Gwamnatin Tarayya a ranar 7 ga Mayu, 2026, bisa zargin haramtacciyar hanya.
Abuja
Samu kari