Abuja
Babban bankin Najeriya (CBN) ya bayyana cewa Zuldal Microfinance Bank ba shi da lasisin gudanar da harkokin kudi a Najeriya, ya ce ba shi da lasisi a hukumance.
Kotun Tarayya da ke Abuja ta samu Nnamdi Kanu da laifi kan tuhumar ta’addanci da gwamnatin tarayya ta shigar, bayan ta ce an gabatar da hujjoji masu ƙarfi a kansa.
Gwamnatin tarayya, jihohi da kananan hukumomi sun raba N2.094trn a watan Oktoba 2025, ƙasa da wannan aka samu a Satumba. Kudin shiga ya karu, VAT ya ragu sosai.
Shugaban kungiyar ta'addanci ta IPOB, Nnamdi Kanu ya birkita zaman kotu yayin da za a yanke masa hukunci kan ta'addanci. Ya ce alkalan kotun ba su san doka ba.
Rikici ya barke a shirin Piers Morgan yayin da Ministan Harkokin Waje Yusuf Tuggar ya musanta zargin cewa ana kisan Kiristoci da gangan a Najeriya.
Sanata Okey Ezea da wasu 'yan majalisar tarayya biyar sun mutu a cikin watanni 18 da suka wuce, wanda ya haifar da babban jimami a majalisar tarayyar Najeriya.
Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta kama daya daga cikin jagororin kungiyar ISWAP, Hussaini Ismaila da laifin ta'addanci bayan DSS ta gurfanar da shi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fasa tafiyar da ya shirya gudanarwa zuwa kasashen waje. Shugaba Tinubu ya dauki matakin ne sakamakon halin da ake ciki a kasa.
Kungiyar ma'aikatan lantarki na kasa baki daya sun yi barazanar dauke wuta a Najeriya bayan zargin 'yan sanda da lakadawa ma'aikatanta duka a jihar Imo.
Abuja
Samu kari