Abuja
Hukumar kididdiga ta kasa, ta bayyana cewa hauhawar farashin kayayyaki ya karu da kashi 34.19% a watan Yunin 2024. Wannan na zuwa ne ana tsaka da rashin abinci.
Yan Najeriya na tsaka da bayyana rashin gamsuwa da yadda Bola Tinubu ke mulkar kasar, sai ga shi an fara shirye-shiryen ya sake tsayawa takara a 2027.
Attajirin da ya fi kowa kudi a nahiyar Afirika, Alhaji Aliko Dangote, ya bayyana cewa ba shi da gida a birnin Landan ko a kasar Amurka. Ya ce haya yake yi a Abuja.
An ruwaito cewa, an ceto wasu adadi cikin wadanda gini ya danne a babban birnin tarayya Abuja. Rahoto ya fadi adadin mutanen da kuma yanayin da suke ciki.
Bidiyo ya nuna yadda Umar Bush ya gamu da Aliko Dangote a fadar shugaban kasa a daidai loakcin da ake cewa ya cika dura ashariya saboda neman suna a intanet.
Jam'iyyar NNPP ta kaddamar da sabon tambarin jam'iyya yayin da ta sha kaye a zaben 2023 da ya gabata bara. An bayyana dalilin sauya tambarin baktatan.
Ana tsaka da cece-kuce kan cewa kusoshin gwamnati ba sa iya ganawa da shugaban kasa, Bola Tinubu, gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya ya samu ganinsa a ranar Juma'a.
Wani ginin bene mai yawa biyu ya rufto a birnin tarayya Abuja. Ginin ya rufto a kan mutane masu yawa. Mutane da yawa sun makale yayin da aka fara aikin ceto su.
Shugaba Bola Tinubu ya sallami Mohammed Bello-Koko wanda Muhammadu Buhari ya naɗa mukamin daraktan hukumar NPA tare da maye gurbinsa da Abubakar Dantsoho.
Abuja
Samu kari