Abuja
Babbar Kotun Tarayya ba ta shirya sake duba hukuncin Nnamdi Kanu ba, binciken CableCheck ya tabbatar da rashin hujja. Lauyan Kanu ya bayyana wannan a matsayin ƙarya.
Sanata mai wakiltar Abuja a Majalisar dattawa, Sanata Ireti Kingibe ta bayyana cewa a shirye take dmta marawa Atiku, Obi ko duk wanda ya samu tikitin ADC.
Gwamnatin Zamfara ta nemi Shugaba Tinubu ya shiga tsakani yayin da take zargin jami'ai daga ofishin Nuhu Ribadu sun 'sace' wani hadimin gwamna, Saleem Abubakar.
A labarin nan, za a ji cewa sojojin Najeriya sun samu gagarumar nasara a lokacin da wasu 'yan fashi suka tare matafiya da ke bin hanyar Abuja zuwa Kaduna.
Hukumar EFCC ta gano makarkashiyar ’yan siyasa na ɓata sunan Ola Olukoyede kafin zaɓen 2027 domin dakatar da binciken rashawa; ta ce ba za ta tsorata ba a yau.
Babbar kotun tarayya mai zama a Abuja ta amince a kwace wasu kadarori da ake zargin na tsohon ministan shari'a, Abubakar Malami ne a Abuja, Kano, Kebbi da Kaduna.
Kotun tarayya ta ba Abubakar Malami belin N1.5bn. Malami zai biya N500m, matarsa N500m, dansa N500m tare da kafa musu wasu sharuda kafin a sake su.
Tsohon Ministan Wasanni, Dr. Tammy Danagogo, ya karyata zargin sa a shirin kashe Ministan FCT, Nyesom Wike, yana mai cewa zargi ne kirkirarre mara tushe.
Rikicin da ya dabaibaye jam’iyyar PDP ya je wajen tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan a Abuja, domin neman shawarwari kan makomar jam’iyyar adawa.
Abuja
Samu kari