Majalisar dokokin tarayya
Majalisar wakilai ta amince da kudirin dan majalisar Cross River, Bassey Akiba na hana masu gidajen haya kara sama da 20% don saukaka wa talakawa.
Wajalisar wakilai ta yi karatu na biyu kan kudirin gyaran dokar hukumar EFCC. Ana son rage karfin shugaban kasa wajen cire shugaban hukumar EFCC.
Majalisar Wakilai ta fara tattake wuri kan kudirin kirkiro jihar Ijebu daga cikin Ogun, an mika shi ga kwamitin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya don nazari.
An yi muhawara mai zafi a Majalisar Dattawan Najeriya kan kudirin dokar zubar da ciki a Najeriya, Sanata Akpabio da Natasha sun yi musayar yawu bayan rufe batun.
Jagoran jam'iyyar NNPP, Olufemi Ajadi Oguntoyinbo ya yi gargadi kan neman dawo da zaben 2027 zuwa 2026. Ya ce lamarin zai kawo matsaloli da dama a Najeriya.
Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin Dr. Aminu Yusuf daga jihar Neja a matsayin sabon shugaban NPC tare da kwamishinoni biyu daga Nasarawa da Yobe.
Shugaba Tinubu ya nada Dr. Bernard Doro daga Jihar Filato a matsayin sabon minista, ya mika sunansa ga majalisar dattawa domin tantancewa da tabbatarwa.
APC ce mai rinjaye a Majalisar Dattawa, bayan wasu ‘yan majalisa sun sauya sheka daga PDP da sauran jam’iyyu. Daga kujeru 59 a 2023, yanzu APC na da sanatoci 75.
Majalisar wakilai ta yi karin haske kan maganar dawo da zaben 2027 zuwa 2026. Hon. Adebayo Balogun ya ce za a dwo da zaben baya ne domin kammala shari'ar zabe.
Majalisar dokokin tarayya
Samu kari