
Majalisar dokokin tarayya







Ma'iakatar ilimin kasar nan ta ce idan aka amince da kudirin gyaran haraji da Bola Ahmed Tinubu ya aika ga majalisar dokokin kasar nan, TETFund zai samu matsala.

Taohon mamba a Majalisar Dokokin Jihar Oyo, Hon. Kehinde Subair ya riga mu gidan gaskiya kwanaki ƙalilan gabanin bikin cikarsa shekaru 60 da haihuwa a duniya.

Gwamna Siminalayi Fubara ya sake tura wasiƙa ga Majalisar Dokokin jihar Ribas, ya buƙaci sake dawowa domin gabatar da kasafin kudin 2025 bayan abin da ya faru.

Gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Tinubu ta soki shirin kafa sabbin jami’o’i 200, tana mai cewa ya fi dacewa a bunkasa wadanda ake da su don inganta ilimi.

Majalisar Wakilai ta amince da kudirorin haraji, ta soke bukatar karin VAT, ta samar da sabuwar Hukumar Haraji ta Najeriya, tare da kafa kotun korafe-korafen haraji.

Majalisa ta yabawa ƙoƙarin rundunar sojoji inda kwamitin kudi ya gabatar da wani muhimmin kuduri don cire harajin kudin shiga na dakarun duba da yanayin ayyukansu.

A ranar Alhamis, 13 ga watan Maris, majalisar dokokin Najeriya za ta sake duba na tsanaki ga dukkanin bangarorin da kudirin harajin gwamnatin tarayya ya kunsa.

Majalisar dattawa ya bayyana takaicin yadda ake ci gaba da samun matsalolin tsaro a sassan kasar nan, wanda ya sa ta gayyaci shugabannin tsaro su bayyana a gabanta.

Jam'iyyar APC ta zama mai rinjaye a Majalisar Dokokin jihar Edo yayin da ƴan Majalisa huɗu daga PDP da LP suka tattara kayansu suka kƙma cikinta.
Majalisar dokokin tarayya
Samu kari