Yan ta'adda
DSS ta gurfanar da tsohon jami'inta Nwaogu Ezeakolam kan zargin shiga IPOB, tallafa mata da yada sakonnin goyon baya, yayin da kotu ta tsare shi a Kuje.
Rundunar sojin Najeriya ta ayyana shugaban ISWAP, Abu Musa Al-Mangawi Baa Shuwa, da mataimakinsa Muhammad Jidda a matsayin waɗanda ake nema, ta sanya ladar kudi.
Mutane 176 da aka sace a harin Woro da Nuku a jihar Kwara sun samu 'yanci bayan watanni, yayin da gwamnatin jihar ta yabawa Tinubu da jami'an tsaro.
'Yan bindiga sun kashe 'yan sintiri uku 'yan uwa a Riyom, Plateau, yayin sintirin dare, lamarin da ya jawo kira ga hukumomin tsaro su dauki mataki.
Ooni na Ife ya tallafa wa cibiyar tsaron Iru Ekun ta Sunday Igboho da Naira miliyan 100 da motar Hilux, tare da kira ga Yarbawa su hada kai wajen inganta tsaro.
Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya shaida wa sojoji cewa ba zai sassautawa masu aikata laifuffuka ba, saboda haka ka da su ragawa duk wani mai laifi.
DHQ ta faɗaɗa tsarin karɓar miƙa wuya ga masu ɗauke da makamai zuwa Kudu maso Gabas da sauran yankuna, tare da tabbatar da babu wa'adin ajiye makamai.
Mutane biyar da ake zargin mayaƙan ƙungiyar ISWAP sun mutu yayin haɗa bam a Marte, da ke Borno, yayin da sojoji suka ƙara matakan tsaro a yankin.
Dakarun Operation FANSAN YAMMA sun dakile harin 'yan ta'adda a Zamfara, sun ceto mutane tara da aka sace, yayin da jami'in soja da ɗan sanda suka rasa rayukansu.
Yan ta'adda
Samu kari