Yan ta'adda
Ministan yada labarai, Mohammed Idris ya ce gwamnati ba ta gurfanar da masu zargin daukar nauyin ta’addanci ba saboda binciken lamuran yana da sarkakiya.
Fasto Elijah Ayodele ya soki Shugaba Bola Tinubu saboda karuwar sace-sace da kashe-kashe, yana cewa idan ya kasa magance tsaro ya kamata ya yi murabus.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya gana da shugaban DSS, Tosin Adeola Ajayi. An yi wa Tinubu bayani game da halin da kasa ke ciki kan lamuran tsaro.
Masani a fannin tsaro, Audu Bulama Bukarti ya bayyana hanyoyi biyar da gwamnatin Najeriya karkashin shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta bi wajen magance rashin tsaro.
‘Yan sanda a Kwara sun karyata bidiyon kama wadanda suka kai hari a cocin Eruku, sun ce labarin karya ne kuma ana ci gaba da aikin ceto wadanda aka yi garkuwa da su.
Hukumar DSS ta tura Nnamdi Kanu zuwa gidan gyaran hali na Sokoto bayan kotun tarayya ta Abuja ta yanke masa hukuncin daurin rai da rai bisa laifin ta’addanci.
Kungiyar Kiristoci ta Najeriya reshen Neja ta la’anci harin da ‘yan bindiga suka kai St. Mary’s Papiri, inda aka sace dalibai, malamai da ma’aikacin tsaro.
A labarin nan, za a ji cewa wasu mutane da ake zargin 'yan fashi da makami ne sun kai hari wani kauye a Kano, inda suka durfafi kasuwar garin, sun yi sata.
Fasto Wilfred Anagbe ya bayyana a gaban Majalisar Dokokin Amurka, yana cewa Najeriya na fuskantar “kashe-kashe masu kama da kisan kare dangi” kan Kiristoci.
Yan ta'adda
Samu kari