Yan ta'adda
Fitaccen dan ta’adda, Bello Turji ya shiga tashin hankali bayan sojojin Najeriya sun kashe kwamandansa, Kallamu Buzu a kwanton-bauna da aka yi a Sabon Birni.
’Yan bindiga sun kashe mataimakin shugaban karamar hukumar Bukuyum a Zamfara, Mu’azu Gwashi, duk da an biya su kudin fansa N15m bayan watanni shida.
Wani wanda ya bayyana kansa a matsayin tsohon hadimin karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle, ya ce ya shirya ba da shaida a gaban kotu a kansa.
Ministan Tsaro Bello Matawalle ya kai ƙara kotu domin dakatar da kafofin yaɗa labarai daga wallafa rahotannin da ke zarginsa da alaƙa da ’yan ta’adda.
Kasar Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar tsaro na shekaru biyar domin karfafa hadin gwiwa ta horo, leken asiri, kera makamai a tsakaninsu.
Sabon kwamandan Operation Fansan Yamma, Manjo Janar Warrah Idris ya gana da gwamna Dauda Lawal a Zamfara. Ya ce za su kawo karshen 'yan bindiga a Zamfara.
Rundunar 'yan sanda a birnin tarayya Abuja ta kama wani mutum da ake zargi da cewa zai saye harsashi ya mika wa 'yan ta'adda a jihar Zamfara daga Abuja.
Manyan shugabannin addinai da gargajiya sun ce tabarbarewar tsaro a Najeriya ta koma gaban Shugaba Tinubu, suna kiran a dauki mataki cikin gaggawa.
Manya a Najeriya ciki har da tsohon hafsan sojoji, Tukur Buratai da tsohon minista, Abubabakar Malami da Godwin Emefiele sun musanta daukar nauyin ta'addanci.
Yan ta'adda
Samu kari