
Yan ta'adda







Rundunar 'yan sandan kasar nan ta yi nasarar hallaka matashin dan ta'adda, Dogo Saleh, wanda aka hakikance ya jawo asarar rayukan jama'a da dama bayan garkuwa da su.

Rundunar tsaro ta dakile harin ramuwar gayya na ‘yan bindiga a Mada, karamar hukumar Gusau, jihar Zamfara inda ta yi nasarar hallaka hatsabibin dan ta'adda.

Wani abin fashewa da ake zargin nakiya ne ya tashi a Borno, inda ya raunata ‘yan sanda uku, yayin da ‘yan bindiga suka kashe yara shida da ke kiwo a jihar Kogi.

'Yan bindiga sun kafa sansani a Bakori, inda suke kai hare-hare. An rahoto cewa suna kokarin mamaye Tafoki, Faskari, Funtua da Danja, inda jama'a ke tserewa.

'Yan bindiga sun kai hari birnin tarayya Abuja inda suka sace wani sarki, jikokinsa da wasu mutane biyar. 'Yan bindigar sun kai harin ne cikin dare jama'a na barci.

Wasu 'yan ta'adda da ake zargin na Boko Haram ne sun kai harin ta'addanci a jihar Yobe. 'Yan ta'addan sun hallaka wani dan sa-kai tare da kona gidaje.

‘Yan bindiga sun kashe ɗan takarar APC, Oluwatosin Onamade, a Legas. Bayan harsashi ya gagara shigarsa, sun sassare shi da adda a kai da fuska har ya mutu.

‘Yan ta’addar Lakurawa sun kashe mutum 13 a Birnin Dede, Kebbi, sun kona kauyuka 7, a ramuwar gayya bayan kisan shugabansu Maigemu da dakarun tsaro suka yi.

Matan Jato Aka sun bukaci gwamnati ta dakatar da kashe-kashe, ta kara tsaro, tare da kawo agajin gaggawa ga 'yan gudun hijira da rikici ya raba da gidajensu.
Yan ta'adda
Samu kari