2023: Shahararren Mawakin Najeriya ya yi nasarar samun takarar ‘Dan Majalisa a PDP

2023: Shahararren Mawakin Najeriya ya yi nasarar samun takarar ‘Dan Majalisa a PDP

  • Jam’iyyar PDP za ta tsaida Olubankole Wellington a matsayin ‘dan takararta a mazabar Eti-Osa
  • Olubankole Wellington watau Banky W zai gwabza da wanda APC ta ba tikiti a takarar ‘dan majalisa
  • Banky W ya yi suna wajen harkar waka da yin fim, ya shiga siyasa da nufin kawo sauyi a Najeriya

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Lagos - Fitaccen mawakin nan ‘dan kasar Najeriya da kuma Amurka, Olubankole Wellington, wanda aka fi sani da Banky W ya samu tikiti a PDP.

Vanguard ta kawo rahoto a ranar Litinin 23 ga watan Mayu 2022 da ya tabbatar da cewa Mista Olubankole Wellington zai yi takara a jam’iyyar PDP.

Banky W shi ne wanda ya lashe zaben fitar da gwani na kujerar ‘dan majalisar wakilan tarayya na mazabar Eti-Osa a jihar Legas da PDP ta gudanar.

Kara karanta wannan

An shiga rudani, wasu sun 'sace' masu kada kuri’a wajen zaben tsaida ‘Yan takaran PDP

A karshen makon da ya gabata ne jam’iyyar PDP ta shirya zabukan tsaida gwani domin fitar da wadanda za su yi mata takarar majalisa a zabe na 2023.

Mawakin yana cikin wadanda suka samu nasara a kan abokan hamayyarsu a jam’iyyar adawar.

2023: Shahararren Mawakin Najeriya ya yi nasarar samun takarar ‘Dan Majalisa a PDP
Tauraro Olubankole Wellington Hoto: @Banky W
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Premium Times ta ce Wellington ya ci kuri’a 28, don haka aka tabbatar da shi a matsayin wanda zai rikewa jam’iyyar hamayyar tuta a mazabar Eti-Osa.

Wannan ne karo na biyu

Idan za a tuna, Tauraron mawakin ya nemi wannan kujera a zaben 2019 a karkashin sabuwar jam’iyyar Modern Democratic Party da aka kafa a 2017.

Mista Wellington ya sha kashi ne a hannun ‘dan takaran da APC ta tsaida, Babajide Obanikoro.

Kwanakin baya sai mawakin ya bada sanarwar cewa ya fice daga jam’iyyar MDP, ya koma PDP da nufin takara a babbar jam’iyya a zaben shekarar badi.

Kara karanta wannan

‘Dan takaran NNPP da ya bi Ganduje, ya janye jiki ya dawo Kwankwasiyya bayan awa 24

Wanene Banky W?

Shekaru kimanin 40 da suka wuce aka haifi Olubankole Wellington a kasar Amurka. Wannan ya sa mawakin ya zama yana da shaidar zama 'Dan Amurka.

Bayan dawowarsa Najeriya ya fara wake-wake tun yana karami a coci. Daga baya Banky W ya gawurta, har ya zama yana cikin fitattun mawaka a yau.

Akwai masu takarar bogi a APC

Dazu aka ji labari Kayode Fayemi ya ziyarci jihar Neja da nufin samun kuri’un ‘yan APC a zaben fitar da gwani na takarar shugabancin Najeriya a 2023.

Tsohon Ministan ya yarda an gagara gyara wuta da inganta tsaro, ya sha alwashin zai magance matsalolin kasar, ya ce shi da gaske yake takara a APC.

Asali: Legit.ng

Online view pixel