Hadimin shugaban kasa, Bayo Onanuga ya ce matsalar tsaron Najeriya bata kai yadda mutane ke yawan fadan ta ba. Ya ce mutane na ruruta matsalar tsaro.
Hadimin shugaban kasa, Bayo Onanuga ya ce matsalar tsaron Najeriya bata kai yadda mutane ke yawan fadan ta ba. Ya ce mutane na ruruta matsalar tsaro.
Rahotanni sun nuna cewa rundunar 'yan sandan Najeriya karkashin Tunji Disu ta yi umarni a binciki sufeton 'yan sanda kan kashe malamar Islamiyya, Ummulkhairi.
Malamin addinin Musulunci a duniya, Dr Zakir Naik ya yi kira ga al'ummar Musulmi su dage da ayyukan alheri a Ramadan. Ya fadi abubuwa 25 da ya kamata Musulmi ya yi.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya kira gwamnan jihar Ondo, Lucky Orimisan Aiyedatiwa, zuwa fadarsa. Kiran na zuwa ne bayan an yi kashe-kashe a taron APC.
Kotun jihar Enugu ta yankewa wani fasto hukuncin kisa kan laifin kashe wani dalibin jami'a. Alkalin kotun ya ce abin takaici ne malamin addini ya kashe rai.
'Yan Najeriya sama da miliyan 1 sun yi rajistar katin zabe da hukumar INEC. Jihar Jigawa ce ta farko, yayin da Legas ta zo ta biyu, Sokoto na binta a baya sai Kano.
'Yan bindiga sun kashe mutane 50 a Tungan Dutse, da ke jihar Zamfara. Mazauna yankin sun ce an yi watsi da gargaɗin su kafin harin ya auku a cikin watan Ramadan.
Ana ta ce-ce-ku-ce game da kudirin da wasu yan Majalisar Amurka suka gabatar wanda ya ambaci Rabiu Kwankwaso a cikin wadanda ake zargi da take hakkin kiristoci.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya zakulo limaman masallatan Juma'a 40, ya ba kowane sabuwar mota domin ci gaba da harkokin yada addinin musulunci.
'Yan bindiga sun kashe makiyaya 3 a Barkin Ladi, Filato a hanyarsu ta komawa gida daga sauraron tafsiri. Kungiyar MACBAN ta zargi 'yan kabilar Berom.
'Yan sandan Gombe sun sassauta dokar tuka babura zuwa 11:00 na dare domin Ramadan 2026. CP Umar Chuso ya ce an tsaurara tsaro don kare masu ibada.
Labarai
Samu kari