Minista Pantami Ya Lashe Lambar Yabon Kirkire-Kirkire na Ilmin Zamani

Minista Pantami Ya Lashe Lambar Yabon Kirkire-Kirkire na Ilmin Zamani

  • Yau kamar kullum, Minista Farfesa Isa Ali Pantami ya samu lambar karramawa daga wajen Shugaba Buhari
  • An karrama babban malamin Addinin kuma masanin ilimin zamani da lambar yabon ilmin cigaban zamani
  • Shugaba Buhari ya ce sam bai yi zaben tumun-dare ba yayinda ya baiwa Malam Isa Ali Pantami mukami a gwamnatinsa

Ministan Sadarwa da Tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ya lashe lambar yabon kirkire-kirkire na ilmin zamani da gwamnatin tarayyar Najeriya tayi.

Shugaba Buhari ya gabatar masa da lambar yabon ne ranar Juma'a, 21 ga watan Oktoba, 2022 a taron karrama ma'aikatan gwamnati da suke nuna jajircewa.

Taron ya gudana ne a fadar shugaban kasa dake Aso Rock Villa, Abuja.

Buhari Pantami
Minista Pantami Ya Lashe Lambar Yabo Kirkire-Kirkire na Ilmin Zamani Hoto: @BUhariSallau1, @FMoCDENigeria
Source: Twitter

Ministan da kansa ya bayyana hakan a bidiyon da ya daura a shafinsa na Tuwita inda ya karbi lambar yabon.

Kara karanta wannan

Pantami, Wike, Jonathan: Hotunan Mutum 44 Da Shugaba Buhari Ya Karrama Yau

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A ranar Laraba, Shugaba Muhammadu Buhari ya taya Ministan Sadarwa da tattalin arzikin zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami, murnar cika shekaru hamsin cir a duniya.

Buhari ya bayyana cewa Malam Pantami na daya daga cikin ma'aikata mafi kwazo, jajircewa da amfani a gwamnatinsa.

A jawabin da mai magana da yawun shugaban kasa Malam Garba Shehu ya fitar, Buhari ce zaben Pantami na daya daga cikin shawari mafi amfani da yayi a rayuwarsa, rahoton TheNation.

Farfesa Isa Pantami zai cika shekaru 50 da haihuwa a ranar Alhamis, 20 ga watan Oktoba, 2022.

An Ware Sheikh Isa Pantami Shi Kadai, An ba shi Kyautar Kasar Waje a Birnin Dubai

A baya mun kawo muku cewa Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani na Najeriya, Isa Ali Ibrahim Pantami ya samu lambar yabo saboda kokarin da yake yi a ofis.

Kamar yadda ya bayyana a Twitter a ranar Talata, 11 ga watan Oktoba 2022, Mai girma Ministan ya tashi da kyautar DWTC a Dubai a kasar UAE.

Kara karanta wannan

Yanzu Haka: Buhari Ya Karrama Jonathan, Wike Da Wasu Mutum 42 Da Lambar Yabo

An ba Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami wannan lambar yabo ne la’akari da ayyukan da yake yi wa Najeriya tun da ya zama Ministan sadarwa a 2019.

Jaridar Science Nigeria tace an karrama Isa Pantami bayan ya gabatar da jawabinsa a game da yadda za a tafi da kowa a harkar sadarwa na zamani.

Pantami ya yi jawabin ne a taron GITEX wanda ake yi yanzu haka a dunkullaliyar kasar Larabawa.

Asali: Legit.ng

Authors:
AbdulRahman Rashida avatar

AbdulRahman Rashida