Latest
Kungiyoyin kwadagon NLC da TUC sun bukaci gwamnatin Najeriya da dakatar dakarin kudin lantarki da kamfanoni suka yiwa yan layin Band A a wasu jihohin Najeriya.
Yayin da ake shirye-shiryen gudanar da zaben jihar Edo a watan Satumba, Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta rusa zaben fidda gwanin jam'iyyar PDP da aka gudanar a jihar.
'Yan sanda a jihar Binuwai sun kama wasu matasa da ake zargi da kone-kone yayin zanga-zanga da aka gudanar ranar Laraba a jihar, kuma zuwa yanzu an kama mutane 18.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar hallaka 'yan ta'adda bayan sun yi musu kwanton bauna a jihar Kaduna. Sojojin sun kuma kwato makamai masu yawa.
Kwamishinan yan sandan Oyo ya sasanta Oba Ghandi Afolabi Olaoye da limami Yunus Tella Olushina Ayilara kan sabani da suka samu a kan zuwa aikin hajjin bana.
Bayan jan kunne da hukumar kula da yanayi ta kasa (NIMET) ta yi kan barkewar ambaliyar ruwa a Najeriya, a jiya ruwa ya mamaye jihar Legas, inda aka rufe shaguna.
Gwamna Douye Diri na jihar Bayelsa ya ce kwata-kwata bai bukatar kasancewa mataimakin Atiku Abubakar a zaben 2027 da ke tafe kamar yadda ake yadawa
Sanata Muhammadu Danjuma Goje ya bukaci shugaba Bola Tinubu ya saka yankin Arewa maso gabas cikin ayyukan titi da gwamnatin tarayya ke kokarin farawa.
Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta bayyana cewa ta gano dubannan matasan kasar nan da ke karyar sun kammala manyan makarantu.
Masu zafi
Samu kari