Latest
Allah ya karbi rayuwar shugaban cibiyar nazari da bunkasa Ilimi ta kasa (NERDC), Farfesa Ismail Junaidu a yayin da ya ke halartar taron kwamitin tuntuba kan ilimi.
Rundunar yan sanda a jihar Bauchi ta cafke Aminu Muhammad da ya shafe shekaru biyu yana damafara da sunan shi soja ne. Ya cuci mutane makudan kudi a jihar.
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya shawarci mazauna babban birnin tarayya da su ajiye maganar zanga-zangar, inda ya ce shugaban kasa zai kawar da yunwa.
Rundunar sojin Najeriya ta sanar da nasara da ta samu kan yan ta'adda a jihar Kaduna. Sojoji sun fafata da yan bindigar inda suka kashe biyu suka kwato makamai.
Domin yaki da masu satar danyen mai da kuma alkinta gidajen man kasar, gwamnatin tarayya ta ce ta kashe dala biliyan 1.5 (Naira tiriliyan 2.36) a cikin shekara 4.
Kungiyar kare hakkin musulmi ta kasa (MURIC) ta yi gargadi a kan wani sabon fim da ke nuna mata a cikin hijabi su na fashi, inda kungiyar ta ce hakan bai dace ba.
Sakataren jam'iyyar APC ya bayyana cewa gwamnatin Bola Tinubu na bakin kokarinta wajen shawo kan matsalolin tattalin arziki yayin da ya musanta rahoton NBS.
Kungiyar Indigenous Youth Leaders ta bukaci Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya hukunta duk basaraken da aka samu da boye masu aikata laifuka a yankunansu.
Yayin da ake shirin fara zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya, Dakta Audu Bulama bukarti ya bayyana hanyoyi biyar da za a bi wajen samun nasara.
Masu zafi
Samu kari