Latest
Gwamna Otti na jihar Abia ya nuna damuwa kan yadda yan bindiga da masu garkuwa suka addabi al'umma inda ya yi gargadi tare da shirin yin garambawul.
Gwamna Monday Okpebholo na Edo ya rushe wasu sababbin masarautu da tsohon gwamna, Godwin Obaseki ya samar inda ya dawowa Oba na Benin, Oba Ewuare II martabarsa.
Kwamitin amintattu na ƙungiyar masu shirya watsa labarai ta Arewa, NBMOA ya shigar da korafin a gaban Babbar Kotun kan Arewa24 da wasu hukumomi saboda saba ka'ida.
Bayan da Shugaba Bola Tinubu ya zama shugaban kasar Najeriya na 16, jam'iyyar APC mai mulki ta lashe zabukan gwamnonin jihohi hudu cikin biyar da aka gudanar.
Kungiyar kwadago ta NLC ta umarci 'yan kungiyar a jihar Jigawa da sun tsunduma yajin aikin sai baba ta gani saboda gazawar gwamnati na fara biyan albashin N70,000.
Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya gargadi matasa da ɗalibai da su guji amfani da miyagun ƙwayoyi, inda ya tuno da lokacin da ya so fara shan taba.
Kungiyar kwadago ta kasa (NLC) reshen jihar Katsina ta yi barazanar shiga yajin aikin sai baba-ta-gani a fadin jihar kan sabon mafi karancin albashi na ma'aikata.
Matatar man Alhaji Aliko Dangote ta rage farashin man fetur ga yan kasuwa domin saukaka musu daga N990 da ta sanar a farkon watan Nuwamba zuwa N970.
Jarumin fina-finan Nollywood da ke Kudancin Najeriya, Stephen Alajemba ya ba maza shawara kan yadda za su yi aure inda ya ce su auri mata uku ko hudu.
Masu zafi
Samu kari