Latest
Gwamna Douye Diri na jihar Bayelsa ya ayyana zaman makoki na kwanaki uku domin jimamin rasuwar mataimakinsa, Sanata Ewhrudjakpo, wanda ya rasu jiya Alhamis.
Sheikh Ibraheem El-Zakzaky ya bayyana cewa bindigogi ba za su taɓa tsoratar da 'Yan Shi'a ba, yayin da ya zargi gwamnati da gaza bin kadin kashe su da aka yi a 2015
Rahotanni sun tabbatar da cewa mutane sun jikkata yayin da wani abin fashewa ya yi bindiga, ya tarwatse da matafiya a kan wani babban titi a jihar Zamfara.
Yunkurin Dr. Abdullahi Umar Ganduje na kafa sabuwar Hisbah mai zaman kanta ya tayar da ce-ce-ku-ce, yayin da wasu ’yan siyasa ke barazanar kai batun kotu.
Hadimin gwamnan jihar Filato ya musanta rade-radin da ake yadawa Gwamna Mutfwang ya sauka sheka daga PDP zuwa APC, ya tabbatar da cewa an fara tattaunawa.
A labarin nan, za a ji cewa Riley Moore, Dan Majalisar Amurka da ya dage a kan batun kisan kiristoci a Najeriya ya koma kasarsa da shirin rubuta rahoto.
Matatar hamshakin dan kasuwa kuma attajirin lamba daya a Afirka, Alhaji Aliko Dangote ta yi rangwame a farashin kowace elitar man fetur ana shirin kirismeti.
Gwamnatin Jigawa za ta kashe Naira biliyan 3.5 domin gyara da inganta harkokin makarantun Tsangaya, wanda ake haddar Alkur'ani Mai Girma a jihar.
Kotu a Abuja ta umarci a tsare tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige, a Kuje kan tuhumar rashawa da almundahana. Za a saurari bukatar belinsa a ranar Litinin.
Masu zafi
Samu kari