Garkuwa da mutane: An sace 14 a jihar Ribas

Garkuwa da mutane: An sace 14 a jihar Ribas

'Yan sanda a Najeriya sun ce an sace wasu ma'aikatan kamfanin mai su goma sha hudu da direbansu a jihar Rivers dake kudancin kasar.

'Yan sandan sun ce wasu 'yan bindiga ne suka tare motar da ma'aikatan ke tafiya a cikinta akan hanyarsu ta zuwa aiki a Fatakwal babban birnin jihar.

Daga baya ne aka gano motar ta su da aka yasar.

'Yan sandan sun ce suna ci gaba da bincike a cikin daji da cikin ruwa, amma har yanzu ba su san ko su wanene suka sace mutanen ba.

Garkuwa da mutane don neman kudin fansa ya zama ruwan dare a yankuna masu arzikin mai a Najeriya.

Mutanen da ake sacewar sun hada da attajirai 'yan kasar da kuma baki 'yan kasashen waje.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: