Muhimman labarai daga jaridun Najeriya

Muhimman labarai daga jaridun Najeriya

Muhimman labarai da sukayi fice daga jaridun Najeriya a yau Litinin 29 ga watan Augusta, domin jin dadin masu karatu.

Muhimman labarai daga jaridun Najeriya

Binciken da jaridar Daily Trust tayi ya bayyana cewa kasar Najeriya ta yi asarar sama da naira triliyan 1.1 a kudin man petir cikin watanni biyar da suka wuce sakamakon harin yan bindiga suka kai a bututunan mai.

An samu akkala hare-hare 25 a bututunan mai daga  ranar 10 watan Fabrairu na shekara 2016 zuwa karshen watan da ya gabata daga tsagerun niger delta avengers.

Jaridar New Telegraph ta ruwaito cewa shugaban kasa muhammadu Buhari ya kuma, shan alwashin maganin yan bindigan Niger Delta kamar yadda gwamnatinsa ta magance yan kungiyar Boko Haram idan suka ki ba da hadin kan tattaunawa da gwamnatin tarraya.

Buhari yace hankalin gwamnatinsa a yanzu ta karkata ga dakatar da lalata tattalin arzikin kasa da yan bindiga keyi a yankunan dake da albarkatun man petir.

Daga karshe Jaridar Daily Sun ta ruwaito cewa gurare da dama sun samu ambaliyar ruwa a jihar Lagas sakamakon ruwan sama da akayi a fadin jihar a karshen mako.

Gurare kamar su Gbagada, Lekki, Oworonshoki, Shogunle, Ikorodu, da kuma Ifako sun samu ambaliyar ruwa sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya, wanda aka fara a daren ranar Asabar har ranar Lahadi. Ya kuma yi asarar dukiya na miliyoyin naira.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng