IMN sunyi zanga-zanga kan tsare Zakzaky, sunyi barazana ga Shugaban kasa

IMN sunyi zanga-zanga kan tsare Zakzaky, sunyi barazana ga Shugaban kasa

-Kungiyar musulman Najeriya, Islamic Movement of Nigeria (IMN), tace zata ci gaba da shirya zanga-zanga har sai shugaban kasa Muhammadu Buhari ya saki shugaban su dake tsare, Sheikh Ibraheem El-Zakzaky

-Kungiyar sunce Zakzaky na bukatar ganin Likita saboda kiwon lafiyar san a tabarbarewa

-Wani malami a cikin kungiyar, Sheikh Bello yace zanga-zangar da akayi a jihar Kaduna a ranar Laraba, 24 ga watan Augusta somin tabi ne kan abunda zai zo nan gaba

IMN sunyi zanga-zanga kan tsare Zakzaky, sunyi barazana ga Shugaban kasa

Kungiyar musuluncin yan shi'a na Islamic Movement of Nigeria (IMN), sunyi barazanar ci gaba da zanga-zanga kan hukuncin gwamnatin tarayya na tsare shugabansu, Sheikh Ibraheem El-Zakzaky da aka tsare ba tare da shari’a.

Sunyi barazanar ne a ranar Laraba, 24 ga watan Augusta lokacin wani zanga-zangan lumana da mambobin kungiyar a jihar Kaduna. Dubunnan yan kungiyar sun shiga zanga-zangan.

IMN sunyi zanga-zanga kan tsare Zakzaky, sunyi barazana ga Shugaban kasa

Hukuman labaran AhlulBayt (ABNA) sun ruwaito cewa shugaban malaman kungiyar IMN, Sheikh Abdulhamid Bello yayinda yake zantawa da manema labarai, a karshen zanga-zangan, yayi Allah wadai da ci gaba da tsare shugaban kungiyar.

KU KARANTA KUMA: CAN ta maida martani kan kisan Kiristoci

Bello yayi kira ga yan Najeriya da su ci gaba da daga muryoyinsu kan rashin bin doka da gwamnatin tarayya keyi inda shugaban kasa zai iya bada umarni kisa , kame da kuma tsare duk wanda ya ga dama saboda ra’ayin kansa.

IMN sunyi zanga-zanga kan tsare Zakzaky, sunyi barazana ga Shugaban kasa
Sheikh Bello yana magana da manema labarai a ranar Laraba, 24 ga watan Augusta

Bello ya kara da cewa kungiyar IMN bazata zanje kiranta kan sakin shugaban sub a, ya bayyana cewa yawan zanga-zangan da sukayi somin tabi ne kan abunda zai zo nan gaba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng