Kaicho! An kama Alhajin Nigeria da goro a Saudia

Kaicho! An kama Alhajin Nigeria da goro a Saudia

-An kama wani alhaji daga Najeriya da goro

-Ma rikon mukamin jakadan Najeriya ya tabbatar da labarin

-Gwamnatin Saudiya ta tanadi tsattsauran hukunci

Jami’an kasa mai tsarki sun kame wani Alhaji daga Najeriya da Goro wanda hukumar ta haramta.

Kaicho! An kama Alhajin Nigeria da goro a Saudia
Wasu mahajjata a yayin da suke shirin tafiya kasa mai tsarki

Rahotannin na cewa alhajin wanda har yanzu ba a bayyana ko wanene ba, da kuma jihar da ya fito, an kama shi ne da ‘yan kwayoyin goron guda 10 a ranar Litinin 15 ga watan Agusta.

Kafar yada labarai ta PM News wacce ta bayar da labarin, ta ce mai riko da mukamin jakadan Najeriya a kasar Saudiyya ne ya tabbatar da afkuwar lamarin, ya kuma kara da cewa, mahunkuntar kasar sun haramta shigo da goro zuwa kasar komai kankantarsa.

Rahotanni na cewa jami’an ofishin jakadancin Najeriya a Jeddah na ta rokon hukumomin kasar da su yiwa alhajin afuwa, domin duk wanda aka kama shi da kwaya zai fuskanci hukuncin kisa ne.

Wani sakon kar-ta-kwana da wani alhaji da ke birnin Madina ya aiko Najeriya, kuma ake ta yadawa a zaurukan sada zumunta na Whatsapp a wayar hannu, ya ce jami’an kasar na caje mahajjata daya bayan daya da na’ura mai kwakwalwa a garin, don gano wanda ke dauke da kwayar magani wacce iri ce, sannan ya yi kira ga wadanda ke tahowa da cewa, kar su kuskura su taho da goro, domin a cewarsa, akwai hukuncin kisa ga duk wanda aka kama.

 

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng