Kasar Amuruka ta fayyace zargin da ake ma Matar shugaba Buhari

Kasar Amuruka ta fayyace zargin da ake ma Matar shugaba Buhari

Gwamnatin kasar Amuruka ta fitar da wata sanarwa dauke da martani zuwa ga Gwamnan jihar Ekiti watau Ayodele Fayose a inda suka tsarkake uwar gidan shugaba Buhari daga zargin da yayi mata na cewa tana da laifi a kasar

Kasar Amuruka ta fayyace zargin da ake ma Matar shugaba Buhari

Haka zalika kasar ta Amuruka ta ce bata neman uwar gidan Aisha Buhari kamar dai yadda gwamnan ya yi ikirari. Shidai gwamnan na Ekiti a ranar wata Litinin 20 ga watan da ya gabata ya rarrabawa manema labarai wani kundin wanda ya ke dauke da sunan Aisha Buhari a cikin jerin masu laifin satar kudi.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa jami'in hulda da jama'a na offishin jakadancin kasar Amuruka a Najeriya Frank Sellin shine ya aika da sakon emel dauke da hakan zuwa ga manema labarai inda ya a ciki ya bayyana hakan. Sellin din ya aike da sakon emel din ne a matsayin amsa ga wani dan jaridar da yayi masa tambaya game da gaskiyar zancen na zargin da Fayose yayi ma Aisha Buhari.

Sellin sai yace: "Bamu da wani bayani game da hakan." A kwanan bayan dai Fayose ya fitar da wani zancen da ya girgiza kowa inda ya ce Aisha Buhari na da laifi a kasar Amuruka kuma ma suna nemanta ruwa a jallo tare kuma da cewa shima Buharin ba wani tsarkakkake ne ba.

Fayosen ya cigaba da cewa: "ai ita ma uwar gidan shugaba Buhari din tana da hannu a cikin badakalar Halliburton. Sadda Kasar Amurukan ta kama Jefferson, ai ya bayyana cewa Aisha Buhari na da hannu a ciki." "Kuna ma iya dubawa akwai sunan ta a cikin feji na 25."

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng