An kama masu neman aikin yan'sanda biyar
-An kama maza biyar a lokacin daukar ma'aikatan yan'sanda a jihar Nasarawa, Lafiya
-An tsare mutanan ne a kan zargin bayar da takardar shaida na jabu da sata
![An kama masu neman aikin yan'sanda biyar An kama masu neman aikin yan'sanda biyar](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt3e58tgd9ihig.jpeg?v=1)
Yan'sanda na jihar Nasarawa, sun kama masu neman aiki biyar, da tuhuma, kan amfani da takardar shaida na jabu da sata, a lokacin daukan Ma'aikatan yan'sanda a jihar Lafiya, a ranar Laraba. An rahoto cewa, hudu daga cikin masu neman aikin, sun bayar da takardan shaida na jabu, domin samun aiki a ma'aikatan yan'sanda, yayinda aka kama cikon na biyar din, da laifin satar wayar salula.
KU KARANTA KUMA: Olayinka na zargin makirci kan chajin shi
Alhassan Mamoda, kwamishinan yan'sanda da ke lura da daukan ma'aikata a jihar, yayi sharhi akan wadanda aka tsare: "Ka kwatanta, tayaya wanda ke neman shiga cikin ma'aikatan yan'sanda, domin kare rayuka, da kaddarorin mutane zai yi sata a gurin da a ke gudanar da tantance ma'aikata.
Ya sace wayar salular, ya kuma boye a cikin wandon sa, an gano shi, an kuma kama shi a lokacin da ake gudanar da bincike. An mika dukkansu a hannun jami'an da ya kamata, domin ci gaba da gudanar da bincike.
A cewar kwamishinan yan'sandan, an tantance musu neman aiki, 5,200 daga cikin mutane 9,627, da suke neman aiki a ma'aikatar, na yan'sandan jihar Nasarawa .
Asali: Legit.ng