An kama masu neman aikin yan'sanda biyar

An kama masu neman aikin yan'sanda biyar

-An kama maza biyar a lokacin daukar ma'aikatan yan'sanda a jihar Nasarawa, Lafiya

-An tsare mutanan ne a kan zargin bayar da takardar shaida na jabu da sata

An kama masu neman aikin yan'sanda biyar

 Yan'sanda na jihar Nasarawa, sun kama masu neman aiki biyar, da tuhuma, kan amfani da takardar shaida na jabu da sata, a lokacin daukan Ma'aikatan yan'sanda a jihar Lafiya, a ranar Laraba. An rahoto cewa, hudu daga cikin masu neman aikin, sun bayar da takardan shaida na jabu, domin samun aiki a ma'aikatan yan'sanda, yayinda aka kama cikon na biyar din, da laifin satar wayar salula.

KU KARANTA KUMA: Olayinka na zargin makirci kan chajin shi

Alhassan Mamoda, kwamishinan yan'sanda da ke lura da daukan ma'aikata a jihar, yayi sharhi akan wadanda aka tsare: "Ka kwatanta, tayaya wanda ke neman shiga cikin ma'aikatan yan'sanda, domin kare rayuka, da kaddarorin mutane zai yi sata a gurin da a ke gudanar da tantance ma'aikata.

Ya sace wayar salular, ya kuma boye a cikin wandon sa, an gano shi, an kuma kama shi a lokacin da ake gudanar da bincike. An mika dukkansu a hannun jami'an da ya kamata, domin ci gaba da gudanar da bincike.

A cewar kwamishinan yan'sandan, an tantance musu neman aiki, 5,200 daga cikin mutane 9,627, da suke neman aiki a ma'aikatar, na yan'sandan  jihar Nasarawa .

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng