An bada hutun ranar Litinin don murnar sabuwar shekarar Musulunci a Osun

An bada hutun ranar Litinin don murnar sabuwar shekarar Musulunci a Osun

Gwamnan jihar Osun, Gboyega Oyetola, ya sanar da ranar Litinin, 9 ga Agusta, a matsayin ranar hutu don murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci - Hijrah 1443 AH.

Wannan na kunshe cikin jawabin da Kwamishanan harkokin cikin gidan jihar, Tajudeen Lawal, ranar Juma'a a Osogbo, rahoton NAN.

Gwamnan ya yi kira ga Musulmai da masu bin sauran addinai suyi amfani da hutun domin addu'a ga cigaban jihar da Najeriya gaba daya.

Ranar farkon sabuwar shekarar Hijra zai kama ranar Litinin ko Talata dangane da ranar da aka ga wata.

An bada hutun ranar Litinin don murnar sabuwar shekarar Musulunci a Osun
An bada hutun ranar Litinin don murnar sabuwar shekarar Musulunci a Osun

Asali: Legit.ng

Online view pixel