Yayin farautar yan bindiga, Sojoji sun kashe mana daruruwan Shanu: Fulani a Nasarawa

Yayin farautar yan bindiga, Sojoji sun kashe mana daruruwan Shanu: Fulani a Nasarawa

  • Shugabannin Fulani sun bayyana yanda harin ya kasance a Ranakun Alhamis da lahadi
  • Kimanin shanu Dari biyar ne suka tarwatse aka rasa inda suke
  • Wasu shaidun gani da ido sun bayyana cewa kimanin shanu Dari ne suka mutu a harin
  • An kaddamar da hare-haren ne tsakanin ranakun Alhamis da Lahadi

Jiragen Sojoji biyu sun hallaka sama da Shanu 1000 a hare-haren da suka kai garuruwan Fulani a kananan hukumomin Keana da Doma na jihar Nasarawa.

Shugabannin Fulani da wasu daga cikin wadanda abin ya shafa sun shaida wa Jaridar Daily Trust cewa an fara kai hare-haren ne tsakanin ranar Alhamis, 10 ga Yuni da Lahadi, 13 ga Yuni.

Wasu matasan Fulani makiyaya da ke kula da shanun sun samu raunuka yayin da ba a gano shanu sama da 500 da suka watsu zuwa makwabtan jihar Binuwai, in ji wadanda lamarin ya rutsa da su.

Wasu majiyoyi sun ce an kashe daruruwan shanu a yankin Giza na Karamar Hukumar Keana a kan dalilin cewa sojoji na aiki don fatattakar ‘yan fashi daga yankunan.

An bayyana cewa aikin daya gudana a ranar Lahadi ya dauki tsawon awanni uku kuma ya haifar da tashin hankali a yankunan yayin da manoma da Fulani makiyaya suka kaurace wa gidajensu saboda tsoron kada a kashe su.

Yayin farautar yan bindiga, Sojoji sun kashe mana Shanu akalla 1000: Fulani a Nasarawa
Yayin farautar yan bindiga, Sojoji sun kashe mana Shanu akalla 1000: Fulani a Nasarawa

"Jirgin da ya gudanar da aikin yana karkashin jagorancin Operation Whirl Stroke na sansanin Sojin saman Najeriya da ke Makurdi a Jihar Benuwe," in ji wata majiya.

"Wasu‘ yan bindiga ne suka harbi jirgin saman soja; wannan shi ne abin da ya haifar da ruwan bama-bamai ga dukkanin yankin. Daya daga cikin bindigogin an zana shi da launukan Sojojin Sama na Najeriya yayin da dayan kuma aka zana shi da launin koren sojoji. ”

Sai dai wasu shugabannin Fulanin sun ce harin ya farune ba tare da wata tsokana ba.

Shugaban riko na kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) a jihar Nasarawa, Bala Mohammed Dabo, ya ce an kuma kashe daruruwan shanu tsakanin Kwatanbala da Akwanaja a karamar hukumar Doma.

A wani hari na daban a ranar Alhamis a Kuduku na karamar hukumar Keana, Alhaji Jigawa ya rasa shanu da yawa yayin mamayar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng