Yanzu-yanzu: Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin sallamar Dr Isa Ali Pantami

Yanzu-yanzu: Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin sallamar Dr Isa Ali Pantami

Majalisar wakilan tarayya ta yi waje da kudirin wani dan majalisa wanda ya bukaci a sallami kuma a binciki Ministan Sadarwa, Dr Isa Ali Pantami, kan zargin alaka da yan ta'adda.

Shugaban marasa rinjaye a majalisa, Ndudi Elumelu, a ranar Laraba, ya yi kira ga majalisa ta bukaci ministar sadarwan yayi murabus ko kuma sallamesa saboda goyon bayan yan ta'addan a shekarun baya.

A zauren majalisan, Elumelu ya ce gabatar da kudirin cewa Pantami yayi murabus ko a sallamesa, Punch ta ruwaito.

Amma Kakakin majalisar wakilan, Femi Gbajabiamila, ya dakatar da shugaban marasa rinjayen inda yace kudurinsa ba ta da alaka da huruminsa matsayin dan majalisa.

Yanzu-yanzu: Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin sallamar Dr Isa Ali Pantami
Yanzu-yanzu: Majalisar wakilai ta yi watsi da kudirin sallamar Dr Isa Ali Pantami
Asali: Original

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng