Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina

Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina

Rahotanni sun nuna cewa mumunar gobara ta ci babbar kasuwar garin Funtua, dake jihar Katsina.

Rahoton Katsina Post ya nuna cewa lamarin gobarar ta ci kasuwar ne misalin karfe biyu na daren Juma'a, 2 ga watan Afrilu, 2021.

Wannan sabon gobara na faruwa yan makonni kadan bayan gobarar da taci kasuwar birnin Katsina.

Wadanda suka shaida aukuwar gobarar Funtua sun bayyana cewa har yanzu ba'a san abinda ya haddasa gobarar ba amma an san inda ta faro.

A cewarsu, anyi asarar kayayyaki na miliyoyin naira.

Hotuna:

Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina
Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina Credit: Katsina Post
Asali: Facebook

Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina
Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina Credit: Katsina Post
Asali: Facebook

Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina
Da duminsa: Gobara ta tashi a kasuwar Funtua, jihar Katsina
Asali: Facebook

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng